content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!: 03/01/2012 - 04/01/2012

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Saturday, March 31, 2012

SARKIN HADEJIA BUHARI DA WAZIRIN SOKOTO A KATAGUM (1)

Image Hosted by ImageTitan.com
HADEJIA A YAU! A lokacinda Sarkin Musulmi Aliyu Bubba ya turo Wazirin Sokoto Abdulkadir Gidado Gurin Sarkin Hadejia Buhari, Wazirin Sokoto shine wakilin sarkin Musulmi a yankin Gabas sai ya taho Hadejia daga Kano Amma sai ya wuce Katagum, Ya turo Jakada zuwa Hadejia yana So su Gana da Sarki Buhari.

Buhari yayi tunanin ya tafi shi kadai daga baya sai ya canza shawara kawai ya Tafi Katagum Da Mutanensa. zasu gamu da Wazirin Sokoto a can. Lokacinda suka isa Katagum Sarkin Hadejia Buhari ya tsaya a Kofar Garin Katagum sai ya tura a fadawa Waziri Ya Iso Wazirin Sokoto da Sarkin Katagum suka zo sai sukace Buhari ya Biyosu amma shi kadai tunda Shawara zasuyi.

Sarki Buhari ya bisu Har ya shiga Kofar Garin Katagum. Sai Mawakinsa wato DAN FATIMA ya fara masa waka yana cewa:-

1, Abubakar Garba Mijin Maza,

2, Buhari kai ke da Nutso Kai ke da Hankali.

3, Don Allah yayi ka Uban Jama'a

4, Kuma kai Allah ya baiwa shugabancin Gidan Sambo

5, Ba dan na isa ba, In ka yarda ga Aike ka shiga dashi

6, Fasa Maza Gagara gasa Aiken shine

7, In ka sauka lafiya ka gaida Na Lara Sarkin Auyo

8, Ka gaida Bello Sarkin Dutse

9, Na Sambo sai ka dawo.

Abinda Dan fatima yake Nufi Sarkin Auyo da Sarkin Dutse duk Buhari ya kashe su. Dan haka shima In ya shiga Katagum Lalle Bazai fito ba.

KodaSarki Buhari yaji Wannan Waka ta Dan fatima sai ya juyo da baya, Wazirin sokoto da Sarkin Katagum da suka fahimci Buhari ya juya sai suka Biyoshi da Ihu Su da mutanen Katagum Suna ce masa Kafiri yaki bin Umarnin Sarkin Musulmi. sai da suka biyoshi har Unik Iyakar Hadejia Da Katagum. kuma sun kashe wasu daga mutanen Buhari. koda yazo Unik sai ya yanke Shawarar ya yi sansani a nan ya koma ya yaki Katagum. kuma mutanensa suka koma suka Karkashe Mutanen Katagum karkashin jagorancin Barde Risku. Daga nan Rashin Jituwa Tsakanin Hadejia da Katagum ya Fara har bayan shekara Goma sha biyu bayan Mutuwar Buhari.

(1863). daga nan Aka samu wasa tsakanin Hadejia da Katagum. koda Katagumawa suka juya sai Wazirin Sokoto ya sake Gyyato Mutanen kano suka Hadu da Na Katagum zasuzo su yaki Buhari. da sarki Buhari yaji wannan Labarin sai shi da mutanensa suka bar Hadejia suka tafi Shabawa Iyakar Hadejia da Gumel Sukayi sansani a can.

da Buhari ya bar Hadejia sai Wazirin sokoto ya nada Wansa Ahmadu Sarkin Hadejia. A shekarar (1850). Wanda dama saboda shi suka Takurawa Sarki buhari.

Tuesday, March 27, 2012

TARIHIN SARKIN HADEJIA UMARU DAN BUHARI 1863-1865:

HADEJIA A YAU!

SARKIN HADEJIA UMARU: A SHEKARAR 1863 allah ya yiwa Sarkin Hadejia Buhari rasuwa a Yakinsu da sukayi da Gogaram (bade). Ko da aka dawo Hadejia aka binne shi sai Manyan fadawan Hadejia wadanda akwai Amana tsakaninsu dashi Buhari. Kamar SARKIN AREWA TATA GANA (GINSAU MAI KINA BAWO) DA KUMA SARKIN YAKI JAJI suka jajirce Sai an Nada UMARU DAN BUHARI SARKIN HADEJIA. kuma hakan Akayi!
SARKIN HADEJIA UMARU NA BIYU an nadashi yana da shekara Goma sha Hudu. Kuma manyan fadawan Mahaifinsa sune suke gudanar da Sarautar tunda shi yaro ne. Kuma a zamaninsa Sarkin Damagaram Tanimu ya kawo yaki Hadejia. Kuma yayi sansani a Arewa da Hadejia daga nan har Jigawar Kasim mutanensa ne. saida yayi kwana Arba'in ana yaki amma Hadejiawa basu fasa wasanninsu na dandali ba. Wata rana ana yaki Sai aka harbi dokin Sarkin Arewa! Koda ya mutu sai akaje gida aka dauko wani Dokin aka cire kayan wancan Dokin aka sakawa wanda aka kawo. Tata gana ya koma kan doki, kashe gari ana cikin yaki sai Tata gana ya sauko daga Dokinsa yayi alwala ya koma kan Dokin, to ashe Sarkin Damagaram yana kallon su sai yace Lalle Sarkin Hadejia ya Isa ana yaki ka sauko kayi alwala? Jiya ma an kashe masa Doki amma saida akaje aka dauko wani a gari? Sai Zagin Sarkin Damagaram yace ai ba Sarkin Hadejia bane Yaronsa ne! Sai Sarkin Damagaram Tanimu yace to Ina Sarkin Hadejian? Sai zaginsa yace ai ance yana gida tunda aka fara yakin nan bai taba zuwa ba. Sai sarkin Damagarm yace wa fadawansa Gobe zamu bar Hadejia kar mu tsaya ayi ta kashemu. Saboda Sarkin Hadejia ya raina mu kwananmu Arba'in amma bai taba zuwa anyi yaki dashi ba? Wa yasan me zai mana in ya zo? Amma basu san Sarkin Yaro bane. Washe gari suka juya suka koma Damagaram. Kuma lokacinda sukazo Hadejia Da kaka ne! Anyi girbi Manoma basu gama Tare Amfaninsu ba. Shi yasa suka dade a Hadejia saboda akwai abinci da ruwa a kusa dasu. SARKIN HADEJIA UMARU Mutum ne mai son Nishadi kowane Lokaci yakan fita Bakin kogi ko Gona Domin Debe kewa. Kuma anyi amfani da wannan Damar inda wata rana ya fita sai aka Rufe Masa Kofa. Koda yazo yaga kofa A rufe sai ya juya ya tafi Chamo ya zauna. Aka nada Kanin Mahaifinsa Sarkin Hadejia Wato HARU BUBBA. 1865-1885. Shi kuwa UMARU DAN BUHARI yayi zamansa a Chamo kuma Ya rasu a shekarar 1920. Allah yaji Kansu Ameen.

HADEJIA A YAU.

Saturday, March 24, 2012

HADEJIA A YAU!: SUNAYEN SARAKUNAN HADEJIA TUN DAGA HABE RULER'S ZUWA YAU.

HADEJIA A YAU!: SUNAYEN SARAKUNAN HADEJIA TUN DAGA HABE RULER'S ZUWA YAU.

SUNAYEN SARAKUNAN HADEJIA TUN DAGA HABE RULER'S ZUWA YAU.

HADEJIA A YAU!
Kamar yanda na baku labari a baya Hadejia anyi sarakunan Habe tun kafin zuwan fulani. A shekarar 11000 aka fara Mulki a Biram wato Garun Gabas, kuma a shekarar 1805 fulani suka fara mulkin Hadejia. Ga sunayen sarakunan Tun daga shekarar 1700 zuwa yau wato 20012.

1, 1700, KANKARAU
2, ASAWA
3, MAMMAN BAKO
4, KAWU
5, BAUDE
6. MUSA
7, 1805 ABUBAKAR

Wadannan sune wasu daga cikin Sarakunan Habe na Hadejia.

A Lokacin sarkin Hadejia na Habe Wato Abubakar fulani sukazo kasar Hadejia, a karkashin jagorancin Ardo Abdure dan Jamdoji, kuma Sarkin Habe Abubakar shine ya basu wurin zama, kuma zamanin Sarkin fulani Sambo suka dawo Inda fadar Hadejia take yanzu. Kafin su kwaci mulki a Hannun sarakunan Habe.

Sarakunan fulani sun karbi Mulkin Hadejia tun daga shekarar 1808 har zuwa yau. Ga jerin sarakunan Fulani..

SARAKUNAN FULANI

1, 1805-1808 UMARU DAN ARDO ABDURE
2, 1808-1808 MAMMAN KANKIYA DAN UMARU.
3,1808-1845 SAMBO DAN ARDO ABDURE. 1st.time.
4, 1845-1847 GARKO GAMBO DAN SAMBO.
5, 1847-1848 ABDULKADIR DAN SAMBO.
6, SAMBO DAN ARDO ABDURE 1848 2nd time.
7, 1848-1850 BUHARI DAN SAMBO. 1st time.
8, 1850-1851 AHMADU DAN SAMBO
9, 1851-1863 BUHARI DAN SAMBO 2nd time.
10, 1863-1865 UMARU DAN BUHARI.
11, 1865-1885 HARU BUBBA DAN SAMBO.
12, 1885-1906April MUHAMMADU MAI SHAHADA DAN HARU BUBBA.
13, 1906-1909 HARU MAI KARAMBA DAN MUHAMMADU.
14, 1909-1925 ABDULKADIR DAN HARU MAI KARAMBA.
15, 1925-1950 USMAN DAN HARU MAI KARAMBA.
16, 1950-1985 june HARUNA DAN ABDULKADIR.
17, 1985-2002 sept. ABUBAKAR MAJE DAN HARUNA.
18, 14 sept. To date. ADAMU DAN ABUBAKAR MAJE.

A RANAR 14 SEPTEMBER 2012 MAI MARTABA SARKIN HADEJIA ALH. ADAMU ABUBAKAR MAJE (C.O.N) ZAI CIKA SHEKARA GOMA (10) YANA MULKIN KASAR HADEJIA.

HADEJIA A YAU!

Thursday, March 22, 2012

HADEJIA A YAU!: TARIHIN HADEJIA A TAKAICE!

HADEJIA A YAU!: TARIHIN HADEJIA A TAKAICE!: HADEJIA- TARIHIN KAFUWAR Hadejia Ya farune daga wani maharbi mai suna Hade, a yawon farauta da yakeyi ne wata rana yana tafe da karyar sa sa...

TARIHIN HADEJIA A TAKAICE!

 HADEJIA A YAU - TARIHIN KAFUWAR HADEJIA Ya farune daga wani maharbi mai suna Hade, shi dai wannan Mutumi Maharbi ne kuma yana yawon farautarsa ne ya taho yankin Hadejia. Kuma a yawon farautar da yakeyi ne wata rana yana tafe da karyar sa sai tayi nisan kiwo har tazo bakin Kogin hadejia, bayan ta sha Ruwa kuma ta shiga ta jika jikinta. ko da tazo sai yaga duk jikinta da ruwa, sai yayi mamakin hakan har ma sai yabi sawunta. Koda yaje sai yaga kogi kuma ga tsuntsaye suna shawagi a gurin. Sannan kuma ya rinka jin kukan Namin Daji, Sai ya yanke shawarar zama a wannan gurin, kuma hakan yayi. Anan ya zauna yayi bukkarsa yake harbe harben Namun daji kuma yayi su wato kamun kifi. In ya kashe namun daji sai yaje ya sayar da fatun. Da kuma Naman. Harma ya dauko Matarsa wato Jia ya dawo da ita wannan gurin. Koda maharba 'yan-Uwansa suka ga Gurinda yake akwai Namun daji da abubuwanda suke bukata sai sukayi shawarar suzo su zauna dashi, sai gurin ya zama Gari Kuma mutane suna zuwa sayen fatu da naman dabbobi a garin. Duk wanda yazo garin sai yayi sha'awar zama a gun, haka nan gari ya fara bunkasa wasu maharba, wasu masinta, wasu kuma mafarauta. Sai gari ya kafu kowa yazo wucewa sai ya yada zango a garin. 

 To kasancewar gari sai da shugabanci ne yasa shi Hade ya zama shugaban garin, duk wanda zaije sayen fatu ko nama sai yace na tafi garin HADEN-JIA. Wato ana masa lakabi da sunan matarsa. To sakamakon takaita kalma irin ta Bahaushe sai aka dunkule sunan ake cewa Hadejia. Kuma bayan zamanin wannan mutumin Hadejia taci gaba da zama gari a Karkashin Daular Biram (Garun Gabas) kuma Sarkin Gabas shine ya Nada Dan-uwan Sarkin Machina Algalfhati ya zama shine Sarkin Hadejia, Shekaru da Dama bayan Hade ya Mutu. Wadannan sune Sarakunan Habawa. Kuma a lokacin akwai kananan Garuruwa masu cin gashin kansu kamar Rinde, yayari, wunti, Anku da dai sauransu. Wadanda suma suna da nasu sarakunan a wannan Lokacin. Amma yanzu duk unguwanni ne a cikin garin Hadejia. 

Hadejia sunyi sarakunan Habe guda talatin da biyu(32) amma sunan mutum uku ake dasu wadanda sukayi mulki kafin zuwan Fulani. 1, BAUDE 2, MUSA 3, ABUBAKAR. Kuma a lokacin Abubakar fulani sukazo kasar Hadejia, kuma shine ya basu masauki a Hadejia Lokacin Hadejia tana karkashin Daular Borno, kuma ya nada Umaru a matsayin Sarkin fulanin Hadejia. Wato kafin Jihadin Shehu usman dan fodiyo. Kuma har yanzu fulanin sune suke sarautar Kasar Hadejia.

MASARAUTAR HADEJIA...... 
Masarautar Hadejia daddiyar masarauta ce wadda ta kafu shekaru da dama da suka gabata, daga lokacin kafuwarta kawo yanzu masarautar tayi fice da kuma yin suna bisa ga muhimman tarihi da take dashi. sannan tana daga cikin masarautun da sarakunan HABE suka mulka kafin Jihadin Shehu Usmanu Danfodiyo, masarautar  tana daya daga cikin masarautun da suke Karkashin Daular Usmaniyya. Daga Gabas tayi
iyaka da Tsohuwar Daular Borno da Gorgaram, daga yamma tayi iyaka da Masarautar Kano, daga Kudu tayi iyaka da Masarautar Katagum sannan daga Arewa tayi iyaka da Masarautar Gumel.

Birnin masarautar yana cikin garin Hadejiya dake Arewa maso gabashin Jigawa a Arewacin Nigeria, sunan garin ya samo asalinsa daga wani Maharbi wadda shine ya kafa garin, wannan maharbi ana kiransa da suna HADE,  yana da matarsa da ake Kiranta da suna JIYA, Sunayen wadannan mutane shi aka hada ya zama HADEJIYA. 
A wancan lokacin mutanen wasu garuruwa in zasu zo sukan ce mun tafi garin Haden jiya, wato ana masa Lakabida sunan Matarsa. Saboda takaita kalma ta Hausawa shine yasa aka hade sunan ya zama Hadejiya.

A wani littafi da Marigayi Tafidan Hadejiya Abdu Maigari ya rubuta ya bayyana cewa
‘‘Shi wannan mutumin da ya kafa Hadejiya wato Hade ya taho ne daga yankin Machina a yawon farauta da yake har ya iso wannan yanki, kuma da ya shigo sai yaga Daji mai Ni’ima da tsuntsaye da namun daji ta ko ina, kuma ga kogi ya fito daga yamma ya gangara zuwa gabas Sannan ga ‘ya’yan
itatuwa kala kala. Da ganin haka sai ya kewaye dajin sosai don ya samu inda ya dace ya zauna, sai ya samu wuri ya kafa Gadonsa irin na maharba yaci gaba da farautar Namun daji da tarkon tsuntsaye’’.

Bayan kwanaki wannan maharbi yana zaune a wannan wuri sai yayi shawarar ya koma ya dauko matarsa don su cigaba da zama a wannan wuri. A lokacin da yayi niyyar komawa sai ya debi abinda zai iya diba na Naman da yayi farautarsa ya dawo garinsu ya dauki matarsa ya koma wannan dajin da yanzu ake kira da suna Hadejiya, sai ya kafa bukkarsa a kan jigawa kuma yaci gaba da farautarsa a wannan wuri har
mazauna karkara dake kusa da wurin suka san da zamansa suke zuwa sayen nama da sauran dabbobin daji. Ana haka ne jama’a suka rinka  zuwa suna kafa bukkokinsu wasu masunta wasu kuma mafarauta da masu kamun tsuntsaye har gari ya zama gari ake kiransa Garun Haden Jiya, sannan akayi shugabanci, zuwa wani dogon lokaci aka takaita Kalmar ta zama Hadejiya. 

Ance a lokacinda ya zauna a Bangaren
Arewa akwai wani gari da ake kira Hadegwaigwai inda yanzu Rubban Dakata take, sannan a bangaren gabas akwai gari da ake kira Kulunfarda inda ada can yake kan hanyar Tandanu. A yamma kuma akwai garin Kadime sannan a Arewa akwai garin da ake kira Majeri, a bangaren kudu kuma akwai garin Tunawa wadda yanzu ake kira Auyakayi. Sannan akwai Kudigin da Hadebako wadda a lokacin take kusa da Kafur, sannan akwai Urki wadda yanzu ake kira Unik sannan akwai Majawa, da kuma manyan garuruwa irinsu Auyo, Garungabas, Kazura, Dawa da Fagi.

A wancan lokacin ance Hadejiya tana Karkashin Daular Auyo ne amma wasu sunce a’a tana karkashin Ikon Garungabas ne tunda daga can ne ake nada Sarki ake kawoshi Hadejia, masu wannan da’awa sun
bada labari kamar haka…

        ‘A zamanin Sarkin Kano Yakubu dan              Abdullahi Barja wadda yayi sarautar
        kano a cikin shekarar (1452-1463),                   Algalfati dan sarkin Machina yaje kano         tare da ‘yan-uwansa guda uku inda                  Sarkin kanon ya bashi sarautar Gaya,            dan-uwansa na farko kuma yaje Rano              Sarkin Rano ya bashi sarautar Dal, na           biyun kuma yaje Zazzau Sarkin                      Zazzau ya bashi sarautar Gayan, na               ukun yazo Biram (Garungabas)  inda              Sarkin Gabas ya bashi sarautar                         Hadejiya.
        Zuriyarsa ne sukayi mulkin Hadejia               har tsawon lokacinda Sarkin Borno Mai        Ali Ghaji ya tura Dansa Mai Idris Aloma        ya yaki kano, sai ya biyo ta Hadejia ya            yaketa ya cinyeta da yaki da sauran                kasashen dake yammacin Borno, sai ya          danka ikon Hadejia da Garungabas da            Dawa da Fagi a hannun Galadiman                Borno, kuma shi Galadiman Borno sai            ya barsu a rarrabe kamar yadda suke            tun farko. Sashen Auyo ya barshi a                  hannun sarkin Auyo, Hadejia ya barta a
        hannun sarkin Hadejiya, Garungabas             ya barta a hannun sarkin Gabas,                     sannan Dawa da Gatare da sauran duk         sai ya barsu a hannun fadawansa,                  amma duk a wurinsa suke karbar                  umarni kuma shi ake kaiwa
       Albarkar kasa har zuwa tsawon lokaci’.

Koda yake ba’a samu rubutaccen tarihi game da sarakunan Habe da suka mulki kasar Hadejiya ba, ance anyi sarakuna guda Talatin da biyu (32), kafin mulkin Fulani. Amma wadanda aka samu sahihin sunansu sune BAUDE, MUSA, DA ABUBAKAR.  Shi wannan Abubakar din shine wadda fulani suka karbi mulki a hannun sa. 

MADOGARA......
1. TARIHIN HADEJIA A TAKAICE. (ABDU MAIGARI. 
2. TURAWA A KASAR HADEJIA. (PROF. H. WAKILI). 
3. THREE NIGERIAN EMIRATE. (VICTOR N. LOW) 
4. MUHAMMADAN EMIRATE. (S. J. HOGBEN) 

HADEJIA A YAU.... 

Saturday, March 17, 2012

HADEJIA A YAU!: A ranar 14 ga watan september 2012; Mai martaba sa...

HADEJIA A YAU!: A ranar 14 ga watan september 2012; Mai martaba sa...: A ranar 14 ga watan september 2012; Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar zai cika shekara goma yana jagorancin kasar Hadejia! A k...
A ranar 14 ga watan september 2012; Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar zai cika shekara goma yana jagorancin kasar Hadejia! A karkashin mulkin Daular Usmaniyya. Zamu rinka kawo muku irin ci gaban da masarautar Hadejia ta samu a lokacin Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar.

Wednesday, March 7, 2012

TARIHIN SARAUTAR SARKIN HADEJIA ALH. ADAM ABUBAKAR MAJE.


Mai Martaba Sarkin Hadejia Alhaji Adamu Abubakar Maje C. O. N.!

Ranar Asabat 3-january-1999, Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje Haruna ya Nada Alh. Adamu Abubakar A matsayin IYAN HADEJIA, NA FARKO. Kuma Ranar Laraba 11-september-2002, Allah ya yiwa Mai martaba Sarkin Hadejia Rasuwa. Alh. Abubakar maje Haruna.

TO A SAKAMAKON AMINCEWA DA GWAMNATI TAYI DA ZABEN 'YAN MAJALISSAR SARKI WATO (KING MAKER'S) Suka zabi Iyan Hadejia Alh. Adamu Abubakar maje a matsayin sarkin Hadejia, Na Goma sha shida (16). kuma an nada shi Ranar Asabat 14-september-2002. Bisa Al'ada ba'a kwana uku ba tare da an nada Sarki ba.

 HAWANSA NA FARKO A MATSAYINSA NA SARKIN HADEJIA SHINE Hawan sallar Azumi wato A watan Disamba 2002. Sannan sallar Layya February 2002 Bai Hau ba saboda yaje Saudiyya.

29-March-2003.

A YAU ASABAT 29-March-2003 ANYI BIKIN BADA SANDA! An baiwa sarkin Hadejia Sanda a Karkashin shugabancin Gwamnan Jigawa ALH. IBRAHIM SAMINU TURAKI! A FILIN WASAN KWALLON KAFA NA HADEJIA WATO (STADIUM).

Kuma bayan an Bashi Sandar jagorancin Kasar Hadejia A karkashin Tutar Shehu Usman Dan fodio, Mai martaba sarki yayi Hawa Guda Uku Wadanda suka Kayatar da jama'ar Hadejia.

1, BIKIN GASAR ALQUR'ANI A SECONDARY FANTAI
2,TARON DA AKAYI A MAKARANTAR KOFAR AREWA
3,SAI HAWAN GANDU WANDA SHIMA YANA DA TARIHI A MASARAUTAR HADEJIA.

Hakiman da ya fara Nadawa sune:- 
1, DAN GALADIMA Alh.babbaji Adamu Hakimin waje. 
2, SARKIN DAWAKI Alh. Umar Ibrahim Hakimin kiri kasamma.
3, KATUKAN HADEJIA NA (2) BIYU Hakimin Turabu. A gaba zan kawo muku Labarin Fitar sarkin Hadejia Rangadi da yayi da kuma Hakiman da ya Nada.