"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Monday, October 29, 2012

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music
HADEJIA A YAU!
Kamar yanda aka sani kasar Hadejia tana Hawan sallah da Hawan Bariki a kowace sallah. Sannan kuma yara suyi Hawan daushe da La'asar.

Kamar yanda Tarihi ya nuna Sarkin Hadejia Abdulkadir shine ya kirkiro Hawan Bariki, a wata fira da mukayi da Galadiman Jauje ya tabbatar min cewa Sarki Abdulkadir mutum ne Mai son Hawa. Kuma shine ya kara hawa ake yin Hawan Bariki, zaije da hakimansa da Dagatai su kaiwa ( Resident) da D.O. Ziyara.
Ranar Laraba 20/April/2005 Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Maje ya kirkiro Hawan Mai Bubban Daki, A sallar Mauludi, wanda kuma za'a rinka yinsa ko wace sallah da yamma. Wato za'a hau washe garin Hawan Bariki.
Ranar Juma'a 22/April/2005, Mai martaba ya hau da yamma. Inda yabi ta tudun mabudi Har zuwa Tudun Barde ya shiga yayi ziyara ga Mai bubban Daki, Bayan ya fito sai yabi ta makera ta Dubantu ta Ganuwar kofar yamma, sannan sai yabi ta bakin kasuwa ta Makwallah ta kofar Jarma sannan In yazo kofar Fada sai ya Tsaya Hakimai kuma su Fara zuwa daya bayan daya suna Jafi. Bayan sun Gama sai ya shiga Gida ya sauka. Hadejia A yau.

No comments:

Post a Comment

RUBUTA RA'AYINKA!