content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!: TAKAITACCEN TARIHIN SHETTIMAN HADEJIA DA M. BILYAMINU USMAN.

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Thursday, November 15, 2012

TAKAITACCEN TARIHIN SHETTIMAN HADEJIA DA M. BILYAMINU USMAN.

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Musichttp://www.MyspaceImageCodes.net">Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music Hadejia A yau! Assalamu alaikum! Barkanmu da shigowa sabuwar shekarar Musulunci. A daidai lokacinda muke kokarin Bankwana da shekarar 2012, Allah cikin Ikonsa wannan shekara tazo mana da wani bubban Rashi wanda bazamu manta dashi ba! Wannan rashin kuwa shine na Alh. Bilyaminu Usman da Alh. Hassan Hadejia (shettiman Hadejia). A ranar Asabat 20/october/2012 Allah yayiwa M. Bilyaminu Usman Rasuwa yana da shekaru 83. Kafin rasuwarsa ya rike mukamai da dama musamman a hukumar Ilmi. M. Bilyaminu ya fara koyarwa a Middle school wato Abdulkadir a shekarar 1948, kuma yayi sakataren Ilmi a Hadejia kuma a shekarar 1976 yayi kwamishinan Ilmi a tsohuwar jihar Kano a lokacin Gwamna Sani Bello. Kuma M. Bilyaminu yayi ministan Ilmi a Jamhuriya ta biyu Lokacin shehu shagari. Kuma ya rike Mukamin Chairman primary Education Board a shekarar 1999. Allah ya kyauta kwanciya. Kuma ya bar mana abin koyi a sha'anin zaman rayuwa, wato Gaskiya da rikon Amana. Ko wadanne Irin darasi muka koya daga Rayuwarsa? Hadejia a yau. http://www.facebook.com/Ismailaasabo Haka kuma Ranar laraba 7/November/2012 Allah yayiwa Shettiman Hadejia Rasuwa Alh. Hassan Abbas, sakamakon 'yar gajeriyar jinya, Shettiman Hadejia tarihin Hadejia bazai manta da irin Gudunmawar da ya bayar ba ta hanyar ci Gaban garin Hadejia da Taimakon Addini, masu iya magana suna cewa ba rabuwa da Gwani ba Maida Gwani. Wannan Haka yake Kasar kago bata Maida Kago. Shettiman Hadejia ya rike mukamin Minista a lokacin Jamhuriya ta daya, bayan nan ya rike mukamin Ministan Man fetur a zamanin Ibrahim Babangida, kuma shine shugaban Kaduna polo club, sannan shine Chairman Board of Directors a kamfanin Leadway Assurance! Sannan Board member A Masallacin sultan Bello dake Kaduna. Allah ya kyauta kwanciya! A cikin abubuwanda ya bari wadanda zamuyi koyi dasu akwai kyautatawa al'umma da taimakawa Addinin musulunci da zumunci. Hadejia a yau. Muna rokon Allah ya bamu Albarkar wadannan mutane, Allah ya maida mana makamantansu, Allah ka kara mana Gaskiya da Rikon Amana da taimakon Al'umma. HADEJIA A YAU.

2 comments:

  1. Allah sarki. Shekarunsu daya, mukaminsu daya, unguwarsu daya, Garinsu daya. Sun mutu a shekara daya! Allah ya gafarta musu.

    ReplyDelete

RUBUTA RA'AYINKA!