content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!: 12/01/2012 - 01/01/2013

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Thursday, December 27, 2012

SAKON GODIYA DAGA MAI MARTABA SARKIN HADEJIA.

HADEJIA A YAU! Assalamu alaikum! Bayan gaisuwa irin ta Addinin musulunci tare da fatan Alkairi. Ina meka godiya da ban gajiya zuwa ga Mai girma Gwamnan Jihar Jigawa da Sanatoti da 'yan -Majalissu da Sarakunan Jihar Jigawa da sauran sarakunan Jihohi makwabta, Game da taya murna da akayi ta cika shekaru Goma a Kan Gadon Sarautar Hadejia! Kuma muna meka sakon godiya ga Jami'an tsaro da Mutanen Gari da Al'ummar Masarautar Hadejia sakamakon Hadin kai da suka bada aka gabatarda taro Lafiya. Allah ya saka da Alkairi. Hadejia A yau.
Kuma Muna meka sakon Godiya da ban gajiya ga Hakimai da Dagattai da Masu Unguwanni na wannan Masarauta mai Albarka. Allah ya saka da alkairi.

Muna kara godiya ga 'yan kwamitin wannan taro wadanda suka bada gudunmawa aka Gudanarda wannan taro Lafiya.

Kuma muna kara Addu'ah Allah ya kawo ci Gaba mai Amfani a Masarautar Hadejia! Allah ya tsaremu daga Masifu da fitintinu a kasarmu baki daya. Ameen. Hadejia A yau!

Friday, December 21, 2012

MAI MARTABA SARKIN HADEJIA (alh. Adamu Abubakar Maje) YA CIKA SHEKARU GOMA A GADON SARAUTA

HADEJIA A YAU! Muna farawa da sunan Allah wanda da Ikonsa ne Komai ya Kasance da kuma Abinda zai kasance! Tsira da Aminci su kara tabbata ga Manzo (s.a.w.) wanda Allah ya aikoshi da zance Mafi dadi wato Alqur'ani.

A ranar Asabat 22/december/2012, Mai Martaba Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar Maje (c.o.n.) zaiyi bikin cika shekar Goma yana Mulkin kasar Hadejia, A karkashin Daular Usmaniyya.

A ci gaba da kawo Muku Tarihin wadanda suka baiwa Kasar Hadejia Gudunmawa wajen ci Gabanta, yau zamu kawo muku Takaitaccen Tarihin Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar Maje. Hadejia A yau!

An haifi Mai Martaba Sarkin Hadejia a shekarar 15/october/1960, a cikin garin Hadejia. Ya fara Makarantar primary a Abdulkadir pri.school Hadejia a shekarar 1967-1972, sannan Ya shiga Makarantar Secondary a Garin Ikot Ekpene Cross-river a shekarar 1973-1976, sannan ya koma Govt.sec.school Danbatta a shekarar 1976-1979.
Mai Martaba Sarki ya samu Nasarar shiga Makarantar Gaba da Secondary ta school of Rural and social science dake Rano ta jihar kano a shekarar 1981-1982, da kuma 1983-1985.

By Ismaila A sabo

Mai Martaba Sarki ya fara Aikin Gwamnati a tsohuwar Jihar Kano a ministry of social wellfare a shekarar 1982-1988, sannan ya koma Kano state pilgrim wellfare board a shekarar 1988-1991.

Bayan da aka kirkiro Jihar Jigawa Mai Martaba Sarkin Hadejia ya koma Jigawa state pilgrim board a shekarar 1991-1998. Sannan ya koma Ma'aikatar Kananan Hukumomi ta jiha a shekarar 1998-1999 Inda ya rike mukamin senior personnel officer.

A wannan shekarar ne Mai Martaba Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje Haruna ya nadashi sarautar IYAN HADEJIA dan majalissar Sarki. Hadejia A yau!
A shekarar 2000-2002, ya rike Mukamin Sakataren Alhazai a Jigawa state pilgrim board.

A ranar Laraba 11/september/2002 Allah yayiwa sarkin Hadejia rasuwa Alh. Abubakar Maje Haruna, sakamakon zaben 'yan majalissar Sarki suka zabi Alh. Adamu Abubakar a Matsayin Sarkin Hadejia Na Goma sha shida (16).

Kuma an Nadashi ranar Asabat 14/september/2002. A karkashin jagorancin Galadiman Hadejia Alh. Habibu Adamu.

A ranar Asabat 23/march/2003, An baiwa Mai martaba Sarki Sanda, a karkashin Jagorancin Gwamnan Jihar Jigawa na wancan Lokacin Alh. Ibrahim Saminu Turaki. Hadejia A yau!

Muna Taya Mai martaba Sarki Murnar cika shekara Goma yana Mulkin Masarautar Hadejia.



Tuesday, December 18, 2012

THE ESTABLISHMENT OF FULANI JIHAD DYNASTY IN HADEJIA (Page one)

HADEJIA A YAU!
In 1808, Sarkin Fulani Umaru, his son and successor Muhammadu Kankiya died. Muhammadu Sambo was appointed as the new Sarkin Fulani of Hadejia. The Fulani leader's In Rinde decide to send a delegation to Sokoto to inform the Shehu of the developments in Hadejia region. Shehu Usman Danfodiyo accept the appointment of Muhammad Sambo as the New Leader of The fulani in Hadejia, condole the people over the death of Umaru and Muhammadu Kankiya, and formally installed Sambo as their new Sarkin Fulani Hadejia. After his formal installation, Muhammadu Sambo decided in 1810 to shift his base from Rinde to Hadejia but before he carried out his plan Habe Ruler of Hadejia Abubakar got the security report of Sambo's intention. Hadejia A yau.

Conscious of the Fulani's military success in the area, Abubakar decided to withdraw from the town without resistence.
Therefore, on the date Sambo decided to occupy Hadejia, on reaching the town, he found the town deserted and so occupied it without any resistance. From that time onwards, Hadejia became the base of the Fulani and eventually the capital of the emirate. An important development that followed the shifting of the Fulani base was the Installation of Sambo as the first Fulani Jihadist Emir of Hadejia in 1810. Thus, Sambo established the first Jihadist dynasty in Hadejia from which sprang all subsquent emirs of Hadejia to date.http://bit.ly/K2WOg4

He also unified all the territories formerly under the Habe administration, under a single central administration to the Emirate of Hadejia. Hadejia A yau!

At the time Sambo moved the Jihadists base from Rinde to Hadejia and formally established the emirate, the structure of the emirate's administration was by far modest andd until mid-century, the capital appeared to have been lesss developed.

At the time of the establishment of the emirate, Muhammadu Sambo relied on a much less formally structured organization and therefore surrounded himself with a relatively small entourage of co-favourite most of whom lacked either titles or fiefs. Therefore, Sambo had to face the difficult task of establishing the apparatus of Centralized administration in his domain. As a firs step towards the establishment of an emirate government, he appointed Yusuf his younger brother as Sarkin Auyo, and his eldest son Muhammadu Garko as Chiroman Hadejia and Makama Lele as the Galadima.
Each of the new title holders was given a specific function to perform in the administration. For example Chiroma, was the crown prince while Galadima was the prime Minister. Sambo's other appointments were those of Madaki (war commander), Ma'aji (Treasurer), Sarkin yari (chief prison supretendant), and Sarkin Wanzamai (chief Barbear). All these state officials were chieftaincy status and performed a specific assignment in the administration. Hadejia A yau!

By Musa Usman Mustapha.

Sunday, December 16, 2012

SABON GWAMNAN KADUNA DA TARIHIN RAYUWAR SA.

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music A yau Lahdi Za'a rantsar da Alh. Mukhtar Ramadan yero a matsayin Gwamnan Jihar Kaduna! An haifi Muktar Ramalan Yero a ranar 1 ga Mayun shekarar 1968 a birnin Zazzau. Ya halarci makarantar Firamare ta karamar hukumar wadda ke Unguwar Kaura daga shekarun 1974 zuwa 1980. Ya shiga ta Sakandire dake Ikara daga shekarun 1980 zuwa 1985, sannan ya wuce Cibiyar Koyon Mulki wadda ke karkashin Jami’ar Ahmadu Bello ta Zaria, inda ya samu takardar shaidar digiri na farko da na biyu, wato Masters, a fannin Akanta daga 1986 zuwa 1991. Ya wuce Kwalejin Koyon Aikin Akanta ta Jos. Muktar ya yi aikin NYSC a jihar Ogun, a hukumar saye-sayen Kayayyaki masu muhimmanci a shekarar 1991. Da ya karasa, sai ya fara aiki sashen Kudi na Jami’ar Ahmadu Bello, a matsayin mai kula da hada-hadar sashen da bankuna. Bayan shekaru biyu, sai ya koma bankin Universal a matsayin mai kula da asusun masu hudda da bankin daga shekarun 1993 zuwa 1997. A wannan bankin saida ya kai matsayin Babban Akantan bankin. A shekarar 1997 ne ya mayar da aikinsa zuwa Kamfanin Nalado Nigeria Limited, kamfanin Namadi Sambo a matsayin Babban Akanta, daga baya ya zama Shugaban Ma’aikata, Shugaban Sashen Kudade da Shugabancin Ma’aikata. Cikin hukuncin Ubangiji, da Namadi Sambo ya zama gwamnan jihar Kaduna a 2007, sai ya nada shi kwamishinan ma’aikatar kudi, mukamin da ya rika shekaru uku. Shi memba ne na kungiyoyi da dama, daga cikinsu akwai Kungiyar Akantoci ta Kasa da Cibiyar Shugabannin Kamfanoni da ta Akantocin Kididdiga da Riritawa Kudade da ta Masu ilmin fasaha da Injiniyoyi da sauransu. Yana da aure da ‘ya‘ya, kuma mutum ne mai sha’awar karance-karance da hawan dawaki da sauraren kade-kade da kuma yin mu’amala da mutane, shi ya sanya yake da tausayi. Wani abin lura shi ne, Muktar Yero ya baiwa marada kunya, inda ya gudanar da ayyukan Ma’aikatar Kudin jihar Kaduna cikin rikon amanar da aka san shi da shi, a duk wuraren da ya yi ayyuka a baya. Saboda haka ne, aka ba shi mukamin mataimakin gwamna a lokacin da Shugaba Namadi Sambo ya zama Mataimakin Shugaban Kasa a 2010. Bayan Mutuwar Gwamna patrick Yakowa Ranar Asabat 15/12/2012. sakamakon Hatsarin Jirgin sama a yau. Alh. Muktar Yero ya zama Gwamnan Jihar Kaduna. An rantsar dashi ranar Lahdi 16/12/2012. ALLAH YA TAYAKA RIKO.

Friday, December 14, 2012

ALHAJI TIJJANI DODO HADEJIA.

Image Hosted by ImageTitan.com 
Hadejia a yau!
A ci gaba da kawo muku tarihin wadanda suka bada Gudun mawa a Kasar Hadejia, yau Aji kima ya kawo mana Kadan daga Irin Gudunmawar da Alh. Tijjani Dodo yake bayarwa!

Dattijo Alhaji Tijjani Dodo Hadejia Dan Baiwa ne, Wanda ba kowa ya san hakan ba.Wannan mutumin baya kasa a gwiwa ganin al'uma sun ci gaba. Wannan yasa ya wajabtarwa kansa fafatawa a harkokin rayuwa daban-daban domin samarwa al'uma mafita. Duk wurin da ka leka zaka hango shi saboda Jajircewa da gina rayuwar sa da yayi akan Gwagwarmaya. 

1.Dan kasuwa ne,

2.Dan siyasa ne,

3.Ba sarake ne,

4.Dan kungiyar aikin gayya ne,

5.Dan kungiyar Achaba ne,

6.Dan kungiyar matasa ne,

7.Dan kungiyar yan kasuwa ne,

8.Dan kungiyar ma'aikatan gwamnanti ne

9.Dan kungiyar kwallon kasa ne,

10.Dan kwamatin hawan sallah ne,

11.Dan kwamatin gyaran makabirta ne.

12.Dan kwamatin jinga ne,

13.Dan kwatin gayaran masallaci

14.Dan kwamatin gyaran gari.

15.Dan kungiyar raya al'adun Gargajiya.


Yanzu haka shi ne shugaban aikin gayya na Hadejia,
shi ne kuma shugaban yan Achaba, haka kuma dogari ne a fadar Hadejia. Lalle Juyi Goma sai Wake Inji masu Iya magana.

A hannu daya kuma dan siyasa,dan kasuwa, Jama'a ya kamata mu jinjinawa wannan bawan Allah, Allah ya bamu dubu masu amfani irinsa.

Wannan hotonsa ne yana bada hannu. Bai yadda yaga abu bai yi iya bakin kokarinsa ba. Idan na magana ne zaiyi idan da karfinsa ne zaiyi idan da aljihunsa ne sai yayi.

Allah ya saka da alherinsa.

Monday, December 10, 2012

TARIHIN SHEIKH JA'AFAR MAHMOOD ADAM.

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music MARIGAYI SHEIKH JA'AFAR MAHMUD ADAM. GIDANSU, HAIFUWARSA DA .TASHINSA. Babban Shehin Malami, Kwararren mai Tafsiri, Gawurtaccen mai Da’awah,Baban Salim Ja’afar dan Mahmoodu dan Adamu, An haifeshi a yankin Daura a jihar Katsina a Shekara ta 1961. Gidansu Malam Ja’afar, Gidane da su ke kulawa da Ilimin Addini da Haddar Alqu’ani, Kakansa ya kasance yana karantar da Littattafan Fiqhu da Yaren Larabci, Wasu cikin ‘Ya’yansa kuma har sun haddace Alqur’ani. Malamin farko da ya fara dorawa Malam Ja’afar karatun Alqur’ani, Wani Malami ne mazaunin gari Daura mai suna Malam Magaji, yana masa matsayin Babban Yaya ne, domin sun hada dangantaka da shi a Kakanninsu, Shine farkon wanda ya fara koya masa Bakaken Larabci, Wannan Malami, Mahaddacin Alqur’ani ne tun a wancan Lokaci. Baban Salim ya fara koyon karatun Alqur’ani ne a hannun Mijin Babbar Yayarsa mai suna Malam Haruna, wanda shima yana masa matsayin Dan’uwa ne, Daga hannun wannan Malamin ne aka maida Malam Ja’afar hannun wani Malamin kuma Dan’uwansa a kauyen Kuza mai suna Baba Rabe, Wannan Malamin shine ya kaurato tare da Baban Salim zuwa garin Kano a shekarar 1971 ko 1972, Sun sauka a gidan wani Gawurtaccen Mahaddacin Alqur’ani dan kasar Nijer ne mai suna Malam Abdullahi dan Zarmu a unguwar Fage a cikin birnin Kano. Baba Rabe yayi fatar ganin Malam Ja’afar ya haddace Alqur'ani tun yana raye, Amma Allah bai so hakan ya faru a Idanunsa ba, Wannan Malamin ya rasu a shekarar 1977 ne, Shi kuma Malam Ja’afar ya haddace Alqur’ani ne a shekarar 1978 DAGA KARATUN ALLO ZUWA JAMI’A Baban Salim ya haddace Littafin Allah mai girma bai wuce da shekara sha Bakwai ba. Ya fara karatun Alqur’ani gadan-gadan ne a hannun Malam Abdullahi Mutumin Nijar, Malami ne da aka san shi da tsanantawa Almajiransa da matsa musu kan inganta haddar Alqur’ani, Ina ganin wannan matsawar ta shafi har Baban Salim, Domin sakamakonta shine wannan ingantacciyar haddar Alqur’ani da Allah ya baiwa Baban Salim, wacce ba kasafai a ke samun Mahaddata Alqu’ani da irinta ba, In ban da ‘yan kadan cikin Tsarakunsa. Malam bai haddace Alqur’ani a hanun Malam Rabe dan Zarmu ba kamar yadda Malamin yayi fata, Dalili kuwa shine Malam Ja’afar da Tsarakunsa a wancan lokaci, wasan kwallon kafa da zuwa kallonta ya dauke musu hankali kan tsayuwar daka kan haddar Alqur’ani, Wannan ya sa, Malam Rabe ya daukeshi daga hanun Malam Dan Zarma ya maida shi garin Hadejiya ya damka shi a hannun wani Malami dan asalin gari Daura amma Mazaunin Hadejiya mai suna Malam Safiyanu,wanda shima Dan’uwa ne ga Malam Ja’afar domin sun hada dangi da shi ta Kakanninsu. Malam Rabe yayi masa haka ne don ya raba shi da kayaniyar Birni da kuma damuwa da Lamarin kwallon Kafa, Maiyiwuwa hakan zai sa shi ya maida hankali kan haddar Alqur’ani, Lalle kuwa hakan ya faru, domin Baban Salin a can ya kamala haddar Alqur’ani bayan rasuwar Malam Rabe. Bayan fara baiyyanar Kungiyoyin Musulunci a Nigeria, Musamman ma Kungiyar Izala, Sai jayayya ta yi yawa tsakanin Mutane kan wassu Mas’aloli kamar ; Hukuncin Salatul Fatih, matsayin Darikun Sufaye, Hukuncin Durkuso a gaisuwa, Sadakar Fida’u bayan Mutuwa, Taron Suna da wassu Al’adun kasar Hausa, Wannan ya tilasta Malam Ja’afar neman Ilimin Littattafai. Malam Ja’afar ya shigar da kansa Makarantu Biyu lokaci guda. Ta farko a wata cibiya ta kasar Masar da ke garin Kano, Ta Biyu kuma wasu Azuzuwa ne da aka bude don yaki da Jahilci. Malam Ja’afar bai shiga Makarantar Firamare ba saboda a wannan lokaci sun yiwa wannan matakin karatun girma. Ya yi karatu a wadannan Makarantu na tsawon shekara Uku a jere daga 1980 zuwa 1983.