content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!: Feb 10, 2012

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Friday, February 10, 2012

HADEJIA A SHEKARUN BAYA!

Hadejia a yau! A shekara arba'in da ta Gabata Hadejia tana da masallacin juma'a guda daya ne, wato masallacin cikin gari. wanda kuma ana zuwa sallar juma'a daga kauyukan kusa da Hadejian a wancan shekarun. kamar Kadume,Arawa,Yamidi,Ganuwar kuka,Hadin mai dan karofi, da sauransu. Da yake zamani juyawa yake kuma jama'a karuwa suke yau a Hadejia akwai masallatan juma'a kusan goma wanda kuma duk wanda kaje kai kace duk jama'ar garin suna can ne. To muna kara godiya ga Allah wanda da ikonsa ne komai yake gudana. Allah ya karo mana alkairi da zaman lafiya. a gaba zan baku labari akan kasuwar Hadejia duk a filin Hadejia a yau.