"" /> HADEJIA A YAU!: Feb 19, 2012

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, February 19, 2012

WAKAR DOKIN SARKIN GUMEL MUHD. SANI. DAGA MALAM AMADU DAN MATAWALLE.

1, Bismillahi rabbana Allah sarkin taimako ka kaini gumel gun sarkin gumel muhammadu sani.



2, Sake shiri muhammadu linzamin duniya uban na makwallah.



3, Na bar Hadejia ran asabat mutane suna ina mallam zaije sai nace Gumel zan jeni.



4, Kuma naje Gumel cikin sa'a sarki na ishe cikin barga tai.



5, Akwa wani doki yana Gumel mai kyau a cikin fada yai daban da dawaki.



6, Doki guda a bakin ran doki goma bidi dan yalawa.



7, Nagarta da kyan gani akwaita a gun bidi takamarsa abar kallo ce wajen rawa mazari ma yasan da bidi dan yalawa.



8, Dokin sarakunan iko ne jirgin saman dawakan lautai.



9, Dokin da ko yana barga tasa indai ka ganshi ka gama kallo.



10, sarkin Gumel uban malam sule kune kuke da mulkin lautai.


Zan kawo muku sauran baiti 5oma a gaba.