"" /> HADEJIA A YAU!: Jun 26, 2012

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, June 26, 2012

RABE DA MUTANEN BORNO


HADEJIA A YAU!
Baramusa wani kauye ne a karamar hukumar Birniwa! Naje ziyara kauyen kuma ganin cewa duk barebari ne a garin, sai na samu damar in tambayi tarihin Rabe dan Fataralle. Na samu wani dattijo mai shekara 76, sai na tambayeshi tarihin Rabe. Kafin ya bani amsa saida ya tsinewa Rabe.
Yace wani mutumin sudan ne wanda ya Addabi bare bari tun daga kukawa Har zuwa Bedde. Sannan yace Rabe ne dalilin zuwansu nan kuma yace duk Babarbare ko bamangenda naganshi a Kasar Hadejia ko wani Guri, to lokacin Rabe ne suka Gudo nan. Yace kamar Kacallari,Kaigamari,kuka Ingiwa,Birniwa.kirikasamma,Jibori, da sauransu duk Gudun Rabe sukayi. A lokacinda Rabe yaje kukawa ya kashe duk mutanen Garin wasu da suka samu labari sai sukayi gudun hijira kasar Hadejia. Wasu kuma suka shigo cikin Hadejia kamar Gagulmari,Kakaburi,zonagalari,kilabakori da sauransu. Yace da can suna da zanen barebari amma yanzu sun canza sai suke zanen a kan fuskarsu wato uku uku. Sauran Labarin sai a Gaba.