"" /> HADEJIA A YAU!: Oct 26, 2012

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Friday, October 26, 2012

BARKA DA SALLAH. (Layya)

Free Web Proxy HADEJIA A YAU! HAWA LAYYA
Yin layya sunnah ce mai karfi da ta kasance
wajibi ga dukkan musulmi. Maza da mata
kowacce shekara. Ta kan fadi a kan mutum in
ba shi da sarari. To ko maras sarari da ya
sauka a wannan shekara ko bai taba hawa
ba . Ya shiga cikin daya daga raguna 2 da
Annabi(s) ya yanka. Ya ce daya nasa ne daya
na masu karamin karfi cikin al'ummarsa har
zuwa tashin kiyama.
Ya tabbata daga ma'abuta ilmi cewa in kana
da riguna 2 ka sayar guda ka yi layya. Annabi
(s) ya ce duk wanda ya ke da dama kuma ya
ki yin layya to kada ya kuskura ya zo wuraren
sallar Idin mu. Annabi(s) ya ce za a ba mai
layya lada kan kowanne gashi guda na adadin
gashin da ke jikin dabbar da ya yanka.