content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!: Dec 14, 2012

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Friday, December 14, 2012

ALHAJI TIJJANI DODO HADEJIA.

Image Hosted by ImageTitan.com 
Hadejia a yau!
A ci gaba da kawo muku tarihin wadanda suka bada Gudun mawa a Kasar Hadejia, yau Aji kima ya kawo mana Kadan daga Irin Gudunmawar da Alh. Tijjani Dodo yake bayarwa!

Dattijo Alhaji Tijjani Dodo Hadejia Dan Baiwa ne, Wanda ba kowa ya san hakan ba.Wannan mutumin baya kasa a gwiwa ganin al'uma sun ci gaba. Wannan yasa ya wajabtarwa kansa fafatawa a harkokin rayuwa daban-daban domin samarwa al'uma mafita. Duk wurin da ka leka zaka hango shi saboda Jajircewa da gina rayuwar sa da yayi akan Gwagwarmaya. 

1.Dan kasuwa ne,

2.Dan siyasa ne,

3.Ba sarake ne,

4.Dan kungiyar aikin gayya ne,

5.Dan kungiyar Achaba ne,

6.Dan kungiyar matasa ne,

7.Dan kungiyar yan kasuwa ne,

8.Dan kungiyar ma'aikatan gwamnanti ne

9.Dan kungiyar kwallon kasa ne,

10.Dan kwamatin hawan sallah ne,

11.Dan kwamatin gyaran makabirta ne.

12.Dan kwamatin jinga ne,

13.Dan kwatin gayaran masallaci

14.Dan kwamatin gyaran gari.

15.Dan kungiyar raya al'adun Gargajiya.


Yanzu haka shi ne shugaban aikin gayya na Hadejia,
shi ne kuma shugaban yan Achaba, haka kuma dogari ne a fadar Hadejia. Lalle Juyi Goma sai Wake Inji masu Iya magana.

A hannu daya kuma dan siyasa,dan kasuwa, Jama'a ya kamata mu jinjinawa wannan bawan Allah, Allah ya bamu dubu masu amfani irinsa.

Wannan hotonsa ne yana bada hannu. Bai yadda yaga abu bai yi iya bakin kokarinsa ba. Idan na magana ne zaiyi idan da karfinsa ne zaiyi idan da aljihunsa ne sai yayi.

Allah ya saka da alherinsa.