content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!: 05/01/2013 - 06/01/2013

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, May 28, 2013

SARKIN DOGARAI DUMAMUSAU...

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU! Buya Mai Komo yana cewa.... Buzuzu baka dadin tauna Dorawa kashe mai zari, yai baki kirin da idanu yai jan idon Barkono, Jakarsa bata rama in ba damo da Macizai. Ya zama Gwanki matattarar 'yan kwari tsumma Madaukar cuta! Shine yakan zama gwanki matattarar Iblisai. Na kumbita kazamin gwarzo, Dan makama ka wuce kushe koda a dajin Gaba. Bawa tsare Sarkinka koda a Dajin Gaba. Baleru baban yaya, Sarkin Dogaran Hadejia, Shine yakan zama Gwanki Matattarar iblisai. Mata kubar kallonsa kayansa babu na zabe. Auya batai laya ba sai malami ya yarda! In malami ya yarda kudi biyan laya ne! Allah ya kyauta Kwanciya...