content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!: KO KUN SAN?........

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, October 6, 2015

KO KUN SAN?........

KO KUN SAN?.....
A shekarar 1971 anyi wata gagarumar yunwa da fari wanda aka sawa suna KWAKWUDUBA, a wannan lokacin hatta fadamu da koguna duk sun kafe babu ruwa, kuma abinci yayi karanci ga mutane. Hakan tasa mutanenmu musamman wadanda garuruwansu yake kusa da Kogi (Masunta) sukayi Kaura daga garuruwansu suka nufi Gabas. Wasu sun wuce har Chadi wasu kuma suka shiga har Kamaru, yayinda wasunsu suka tsaya a garin Baga.

Koda yake a lokacin wannsn garin da ake Kira Doran Baga mutanenmu ne suka je suka kafa Daba a kusa da gabar Kogi. Anan ne sukaci gaba da zamansu suna Kamun Kifi da sauran Albarkatun ruwa sannan su sarrafa su kawo Maiduguri da wasu sassa na jihar Yobe su sayar. Haka gari yaci gaba da girma sakamakon zuwan mutane Masunta domin su samu abinda zasuci da Iyalensu. Sakamakon gari ya zama gari har sai ake kiran Dabar tasu DORON BAGA.

Akasarin mutanen da suka tafi daga kasar Hadejia mutanen Kafinhausa ne da kuma yankunan Kirikasamma da Guri, idan ka lissafa wancan lokacin zuwa yau zai baka shekara 44. Wadannan mutanen wasunsu sun bar garuruwansu ba tare da suna dawowa suna gaida Iyayensu ba, wasunsu kuma har iyayen nasu suka bar Duniya basuzo sun gansu ba,wasu a cikinsu sun manta yanda yanayin garinsu ma yake saboda sun samu Duniya acan. Da yake ba duk aka taru aka zama daya ba wasu sukan zo su gaida 'yan-uwansu da abokan Arziki sannan su koma tunda Allah yayi zamansu acan.

RIKICIN BOKO HARAM....
A cikin Shekarar 2008/2009 Rikicin Boko Haram ya faru a Gabashin Nigeria, musamman yankunan Jihar Borno da Yobe da wasu sassa na Adamawa da Bauchi da Gombe, wanban rikici yayi Asarar Rayuka da Dukiyoyi masu dinbin yawa, inda akayi ta kone Gidaje da Kasuwanni da wuraren Sana'a. Wannan ne yasa wadancan mutane da na Ambata a sama wadanda Kwakuduba tasa suka bar garuruwansu sai suka fara tunanin su dawo gida, sakamakon fadin Hausawa " Giji Lahira ce" anan ne fa suka fara dawowa ba tare da abinda suka tara a can ba, wasu sun dawo gida sun tarar duk wadanda suka sani sun mutu wasu kuma tsufa ya kama su.

No comments:

Post a Comment

RUBUTA RA'AYINKA!