content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!: 10/01/2016 - 11/01/2016

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, October 30, 2016

TARIHIN GARIN BARNO (MAIDUGURI)...

HADEJIA A YAU!
        
Mutanen  Barno suna da yawa qwarai, ita kuwa Barno tana kusa da Tafkin Chadi ne, wannan Tafki yana da ban mamaki qwarai don baya da zurfi har mutum yana iya tuqa kwale-kwale ya ratsa Tafkin na Chadi saboda Ruwan Kogi kaxan yake shiga Tafkin kuma iska tana hura shi daga gefe zuwa gefe. Da ka matso kusa da Tafkin sai kayi ta ganin abin mamaki, in kana gabar tafkin bazakaga Ruwa ba sai kayi ta ganin Ciyayi har fiye da Mil biyu gabanka. Mazauna wurin Larabawa ne da suka Dogara da tafkin don rufawa kansu Asiri. In ka duba kewaye da tafkin sai kaga kasa ce shimfidaddiya, ta ko ina kuwa shimfidaddiyar kasar nan ta kai Mil dari da wani abin, amma in ka matsi tafkin sai kaga gangara kadan zuwa tafkin. 

Wannan shimfidaddiyar kasa ta zama kamar hanya tsakanin  kasashen Afrika ta yamma da tsakiyar Afrika da Dafur da kuma kwarin kogin Nil. Ta nan ne matafiya na Afrika na shekaru suke wucewa. Hanyar nan tana da wuyar bi amma bata da wuya kamar hanyar da take Arewacinta, wadda sai an ratsa Hamada ko wadda sai an bi tsakanin Duwatsu  daga kudu. Wurin nan kana ma kamar fadama lokacin Ruwa, amma kuma in Ruwan ya janye ana iya wucewa. Iyakar saninmu wadansu mutane ne an ace musu ‘SO’ suka fara ama a wurin nan, kuma ana cewa mutanen suna da Girman jiki da tsawo kamar wadanda suka fara ama a Kano. Amma cikin Tarihi abinda aka iya samu nasu shine manya manyan Tukwane, wadda akace matansu suna dibar Ruwa dasu. Tukwanen suna da nauyi har sai mutane da dama sun hadu zasu iya daga su daga wurin da suke. Kowace Tukunya kuma tayi misalign kafa biyar a tsaye, wadannan mutane a Gabar Tafkin Chadi suka zauna. Babu dai wadda yasan daga inda suka fito, kuma da wuya a kara gano wani abu game dasu, sai dai in an kara hako irin abinda suka bari…


WADANDA SUKA FARA MULKI A WURIN….
Wadanda suka fara mulki a kewayen Tafkin Chadi, wadansu mutane ne ana ce dasu SEF. Asalinsu kuwa Berber ne, watakila sunzo ne da kansu ko kuma sun hade ne da mutanen da sukazo daga kudancin Bahar Rum ne. sune suka kafa Mulkin Kanem, suka zauna sukayi mulki a wurin yau misalin Shekara 1,225 kenan da suka wuce, sai wasu Kabilu suka kara zuwa suka zauna har suka kara girman wurin. Cikin 1250, shekara ta 697 kenan Dunama  Dabalemi, Mai na Kanem ya mulki makekiyar kasa wadda tun daga Kogin Nil taa kai Kogin Kwara, har wani yankin Hamada Kasar nan ta mamaye. Daga Fezza (A Kudancin Tarabulus) har Duwatsun nan na Mandara na kudu da Chadi duk kasarsa ce. Kasarsa tayi iyaka da Songhai wajen kogin Kwara, har dai kasar Hausa duk cikin Kasarsa take a da. Masu mulkin wannan kasa suna saduwa da masu mulkin kasar Masar da Tarabulus harma wakilan waccan kasar suna zuwa wannan kasar don wani muhimmin Al’amari. A lokacin nan ana tsammanin Kanuri wadda Hausawa ke kiransu Barebari, sun gauraya da wasu kabilu ne daban. Ana tsammani su Kanuri tare sukazo da kakannin kakannin Hausawa.

Bayanda masu mulkin Kanem watau Sef, suka kaura sai suka koma kano, bayan shekara saba’in (70) sai Mai Ali Ghaji ya sake kafa wani mulkin amma a yammacin Chadi ya kafa. Bubban Garinsa shine Birnin Ngazargamu, yanzu garin ya zama kango amma da ganin kangon Garin kasan bubban gari ne. misalin shekara dari uku (300) da suka wuce anyi sarakuna masu hikima a Barno, kamar yadda akayi a sauran kasashe. Cikin Sarakunan Barno akwai wani wai shi Idris Alooma, yana da wani Malami wadda ya rubuta labarai iri iri na lokacin nan, wadda da taimakonsu muna iya gane abinda ya faru a lokacin nan. Amma a lokacin nan Barno ba kamar Barnon da muka sani a yanzu take ba, lokacin nan daga Nguru sai ka fada kasar Hausa. Nguru  tana da muhimmanci kwarai a Daular Kanem, saboda haka sai aka damkata ga Galadiman Barno, daya daga cikin manyan Hakiman Barno…..

       FULANI SUN YAKI BARNO……….
Fulani sun baiwa Barno Kashi har fiye da yadda suka ba Kasashen Hausa, Fulani sun ci Bubban Birnin Kanuri. Koda yake Kanuri sun kori Fulani amma daga baya sun dawo, to da suka sake dawowa sai Mai na Barno ya nemi Taimako daga Kanem. Muhammad Al-Amin El-kanemi wadda aka fi sani da Shaihu Laminu, shine shugaban wadanda sukazo taimakon nan. Shi Shaihu Laminu Haziki ne kwarai, kuma yana da Ilmi mai yawa. Ya taba zuwa Hajji kuma ya taba zama a Masar, lokacin da zaizo yayi ta Gargadi ga mutanen Kanem don suzo su taimaki mutanen Barno. Da sukazo kuwa sai suka samu sa’a suka kori Fulani, amma Fulani basu dade ba sai suka sake cin Birnin Ngazargamu a cikin shekarar 1810. Har yanzu Shaihu Laminu ya sake zuwa Taimakon Kanuri, a wannan lokacin sai ya gayyaci Larabawa suka taimakeshi ya sake korar Fulani. To sai Shaihu Laminu ya zauna a Kukawa, koda yake Sarakunan Barno suke kula da Al’amarin kasar, dukda haka Shaihu Laminu shine Uban kasar Barno.
Umaru dan Shaihu Laminu shine ya gwada sosai don yana so yazama Mai na kasar Barno, amma Mai na karshe wani yaro dan shekara Goma sha bakwai (17), yayi kokarin hana Umaru ya zama Mai. To sai yaki ya tashi, Yakin nan fa shine karshen Sarakunan nan da akayi a Barno daya na bin daya har misalign shekara dubu (1000).

  SHIGOWAR RABEH AZ-ZUBAYR……
Cikin shekarar 1893 sai Rabeh yazo daga Sudan da shiri na gaske, ya afkawa Barno nan da nan yayi Karin kumallo da ita. Allahu Akbar! Cikin yakin nan ne aka kashe Kakan Shaihun Barno na yanzu, wajen shekara shida (6), Rabeh da mutanensa sai abinda sukaga dama a Barno. Wani yaki da akayi a kusa da Farlomi, nan faransawa suka kori Rabeh har suka kashe Dansa Foldlellah. Bayan lokaci kadan sai Ingilishi suka ci kasar da yaki kuma suka mayar da zaman Lafiya da Salama. 

   RIKICIN BOKO HARAM......... 

Saturday, October 15, 2016

BUPOLY HADEJIA... TRIBUTES TO PROF. M.A.HUSSAINI. By Auwal Abu Daud.

HADEJIA A YAU!


The narratives of Binyaminu Usman College of Agriculture, Hadejia now Binyaminu Usman Polytechnic, could not be complete without identifying with the former Provost and Rector.
Prof. Muhammad Auwal Hussaini . The
journey begins four years ago, precisely on 19th September, 2012 when he took over as the 2nd Provost of the former autonomous College of Agriculture. His arrival at the scene brought hope and revolutionized the institution to stand tall among its contemporaries.

Prof. M.A.Hussaini as erudite professor
of Agronomy brought his wealth of experience to bear on every sphere of the institution. He came at a time when the College was desperately in need of
leadership with vision to frontally steer the ship of the crisis ridden institution which clearly manifested in low students’ enrolment, low teacher to students ratio, obsolete equipment, low staff moral and a kind of generalized hopelessness. To his credit within shortest time the scenario changed for better. The manifestation of his good leadership style could be recognized through modest achievements recorded in the following areas:

1. Increasing number of academic staff: The academic staff was strengthened by
54.76% rise by recruitment of competent and dedicated staff through open and transparent process for the first time in the history of the College; from 38-84 academic staff.
2. Establishment of new academic programmes: the number of academic programmes of the institution were rised from four(4) National Diploma
programmes to nine (9), 55.55% increase. Also 0-5 Higher National Diploma (HND) programmes were equally established. Eight (8) programmes were granted interim accreditation by National Board for Technical Education (NBTE).
3. Provision of laptop computers to all
academic staff and strategic non- academic staff through National Communication Commission (NCC) ICT
support scheme.
4. Digitization of Student Record and Staff Management System by establishing first website and portal of the institution. 
5. Digitization of admission process, results processing and examinations management.
6. Establishment of Management Information System Unit (MIS) for the institution.
7. Provision of Wireless Internet Service at the institution library.
8. Reinvigorating the institution’s animal farm by providing necessary facilities.
9. Establishment of functional poultry
farm for the institution.
10. Establishment of standard orchard
11. Establishment of Date Palm plantation.
12. Establishment of Moringa plantation.
13. Establishment of Neem Tree plantation at new campus of the institution.
14. Establishment of Guava plantation.
15. Completion of new site of the institution with state of the art facilities.
16. Establishment of modern Digital Metrological Station (DMS).
17. Regular payment of staff development packages.
18. Regular supply of staff welfare package
19. Establishment of Staff Welfare Committee (SWC).
20. Establishment of fish farm and hatchery.
21. Regular training and retraining of staff on areas of strategic interest to the institution.
22. Speeding process of result collection.
23. Landscaping of major roads at new campus.
24. Providing mentorship to staff.
25. Drastically reducing corruption in
admission and examination through the use of Information and Communication Technology (ICT).
26. Establishment of Monthly Bulletin
for the institution in order to improve image of the institution. And above all, on 15th January, 2016 the College was upgraded to status of a Polytechnic by the Jigawa State Government.

Prof Dedication to work is uncommon as he demonstrated by coming to office
regularly; from Monday to Friday sometime even on weekends.
These traits really had endeared him to
many. Unlike contemporary Africans, when his first term was coming to an end many people encouraged him to seek for second term but he told them that he has done his best to the institution and therefore there is need for him give chance for somebody to try and consolidate on his gains. The Polytechnic community will certainly miss his humbleness and dedication to service.

As you retire as our Rector we fervently pray that May Almighty Allah reward your meritorious service to your state and your country and may he give you good health and strength to continue to render selfless service to humanity.
Thank u sir. 

Wednesday, October 12, 2016

THE SHETTIMA OF HADEJIA, BARRISTER IBRAHIM HASSAN HADEJIA. By Muhammad Lawal Yahya.

HADEJIA A YAU!

THE DEPUTY GOVERNOR BARRISTER IBRAHIM HASSAN Born in 1965 into the family of late elder statesman, Alhaji Hassan Hadejia who was until his death, the Shetima of Hadejia, the present Deputy Governor. 

 Barrister Ibrahim Hassan went through the Sacred Heart Primary. School, Kaduna, Barewa College Zaria, School of Basic Studies, ABU zaria, from where he was enrolled into the Faculty of Law, Ahmadu Bello University, Zaria, and the Nigerian Law School Lagos after which he was called to the Bar. He later went to the Department of Continuing Education, at the Oxford University, United Kingdom where he obtained a Diploma in Computing in 2005 Between 1990 and 1999 after serving as a Youth Corper, with the Nigerian Telephones and Transmission, Iganmu, Lagos, as Marketing and dealer relationship manager. 

 Barrister Ibrahim worked at the Credit and Finance Ltd as Company Secretary and legal Adviser as well as Head Recovery Task Force, Liberty Merchant Bank plc, Head Credit Administration, Head Foreign Operations, Member Task force on migration of Bank’s Software from Bancmaster to Kapiti and AS400 environment, Foreign Exchange Dealer, Manager Port Harcourt Branch; responsible for Eastern Region, most profitable branch 3 years in a row, Head International Treasury and Chief Foreign Exchange Dealer, with direct responsibility for a trading open position limit of $5 Million daily.

In 1999 he became the Attorney General and Commissioner of Justice, Jigawa State, a position he held until 2000 when he was appointed the Secretary to the State Government from where he subsequently rose to the position of Deputy Governor in 2002 until 2007 when the Government handed over to a new administration. To his credit during his first coming, Barrister Ibrahim Hassan was responsible for ensuring the inclusion of Jigawa State as one of the 6 DFID focal states, leading to the establishment of the SLGP program (State& local Government Program) in the state and 4 subsequent DFID supported programs namely, PATHS(Partnership for transforming health systems, JEWEL (Jigawa Wetlands livelihood Program) and the Access to Justice Program, introduced and established Integrated Financial Management Information Systems (IFMIS) to accommodate unified budgeting and link the budget ministry with the State treasury and Salaries and pensions department, and organized and produced the Jigawa SEEDS document (J-SEEDS) and translated abridged versions in English & Hausa and a 13 episode Hausa radio drama series to explain and disseminate J-SEEDS as well as supported the production of LEEDS for 9 out of 27 local governments. He also chaired the DFID financed State and Local Government Program (SLGP) to facilitate the implementation of reform in State and Local Government policies and successfully re-organized contracting and tendering process through the reorientation and repositioning of the Finance & General purposes committee (FGPC) and the establishment of the Project Monitoring and Evaluation Unit (PMU). He is a member of the Nigerian Bar Association, and the chartered Institute Of Arbitration, United Kingdom. 

His hobbies include reading, Web research and data mining, squash, and to cap it all,  the Barrister is a Computer adept, proficient in all Microsoft Office applications, Comfortable with both Windows and Mac OS LAN Administration (AS400, NT, Novell) java programming. He is married with children.

Saturday, October 8, 2016

GALADIMAN HADEJIA USMAN.....Daga Suleiman Ginsau.




NAZARI AKAN TARIHI DA RAYUWAR GALADIMAN HADEJIA ALH. USMAN ABDUL'AZIZ. (USMAN II)

(TARE DA SULEIMAN GINSAU)

"SALSALAR HAIHUWA DA KARATUN GALADIMA"

Kamar yadda yake a bayyane an haifi Mai Girma Galadiman Hadejia Alh. Usman Abdul'aziz a cikin garin Hadejia da ke Jihar Jigawa a ranar 23 ga watan Oktoba a shekara ta 1959, wadda yayi dai-dai da 20 ga watan Rabi'ul Sani na shakarar ta 1379. Idan muka dubi rayuwar Galadima a bangaran karatunsa ya halarci Makarantar Hudu Islamiyya dake garin Hadejia a shekarar 1963, ya halarci Makarantar Firamare ta Hadejia Central a cikin shekarar 1965-1971, inda daga nan kuma ya wuce zuwa Kwalejin Geamnati dake Kano wadda a yanzu ta koma Rumfa Kwalej a shekarun 1972-1976, a matakin sakandare daga nan kuma ya wuce Makarantar koyan sana'a dake Kaduna (Kaduna Polytechnic) anan ne ya yi karatunsa na Karamar Diploma ckin shekarun 1976-1979. Yayi Babbar Diploma akan kasuwanci a (Kaduna Polytechnic) cikin shekarun 1979-1981. Yaci gaba da karatunsa a Jami'ar Abubakar Tafawa Balewa Bauchi a Shekarun 1997-1998 ya sami shaidar Babbar Diploma ta gaba da Digiri a kan kasuwanci, daga nan ya wuce kasar waje domin karo Ilmi inda ya shiga Jami'ar St. Clements da ke kasar Australia a shekarun 1998-1999 a inda ya samu shaidar Digiri na biyu a bangaren Kasuwanci, daga nan ya sake komawa Jami'ar Tafawa Balewa dake Bauchi domin cigaba da karatunsa a inda ya sake samun shaidar wani Digirinsa na biyu a kan kasuwanci na komai da ruwanka wato ( General) a shekara ta 2000-2001. Mai Girma Galadima Usman Abdul'aziz ya yiwa kasa hidima a Jihar Binuwai. daga shekara ta 1981zuwa1982 (Taskar Suleiman Ginsau)



"RAYUWARSA TA AIKI"

Bangaran Rayuwarsa ta aiki kuwa abin abin sha'awa da ban mamaki Mai Girma Galadiman Hadejia Alh. Usman Abdu'aziz ya fara aiki ne a ma'aikatar Ciniki da masana'antu ta tsohuwar Jihar Kano a shekara ta 1982, a matsayin jami'i mai kula da bangaren ciniki.

"AIKIN GALADIMA A KAMFANIN TOTAL"

Daga nan ya kama aiki da Kamfanin Mai na Total a matsayin wakili mai kula da harkokin kasuwanci a watan Augusta na shekarar 1983, bayan samun horo da yayi a Hedikwatar Kamfanin da ke birnin Lagos, daga nan an yi masa canjin aiki zuwa Jihar Kano a matsayin jami'i mai kula da harkokin kasuwanci.

Bayan dawowarsa Kano ansake yi masa canjin aiki zuwa Jihar Barno a shekarata 1988 a matsayin wakilin harkokin kasuwanci mai kula da shiyyar Arewa maso Gabas na Kamfanin Mai na Total. Kasancewarsa a wannan shiyya ya bada gagarumar gudunmawa wajen cigaban wannan Kamfani, hakan ne ya sanya aka sake yi masa canjin aiki zuwa sabon ofishin da aka bude na Kamfanin a Jos, hedkwatar Jihar Filato a matsayin Manaja mai kula sha'anin kasuwanci, zamansa a Jos ya gudanar da ayyukan da suka kai Kamfanin ga samun nasara, a inda aka daga darajarsa a wannan shiyya, hakan ta sa aka kara ciyad dashi gaba aka bashi Manajan kula da kasuwanci a shiyyar Arewa maso Gabas, a shekara ta 1996. A lokacin da yake gudanar da ayyukansa a wannan shiyya a Jos bayan ci gaban da na bayyana mai dorewa ya samar ta fuskar habaka kasuwancin Kamfanin. Lallai Galadima ya tabbatar wa Duniya cewa shi tsayayye ne wanda yasan harkokin kasuwanci bisa gaskiya da rikon amana.

Har ila yau kwarewarsa ce ta sa aka sake karama masa mukami zuwa Manajan yanki wanda ya kunshi Jahohi kamar su:-
1. Bauchi
2. Gombe
3. Barno
4. Yobe
5. Adamawa
6. Taraba
7. Filato
8. Nasarawa
9. Binuwai
10. Kogi
shedikwatar tana nan a matsayinta a Jos. 



A shekara ta 2001 lokacin da Kamfanin Mai na Total da na ELF suka hade an sami canje-canje inda aka kirkiro sabon Ofis mai kula da Arewa mai nisa dake da shedikwata a Kano, tare da nada Galadima a matsayin Manajan shiyya mai kula da Jihohin da suka yi iyaka da kasashen Republic of Benin, Niger, Chad da Cameroon kamar haka:-
1. Kebbi
2. Sakkwato
3. Zamfara
4. Katsina
5. Kano
6. Jigawa
7. Yobe
8. Barno
9. Adamawa
A shekarar 2006 an kuma yi masa canjin aiki zuwa birnin Benin a matsayin Manaja mai kula da shiyyar yamma ta tsskiya. Kamfanin Total ya kirkiro Ofishin kasuwancin Najeriya a Abuja wanda aka bawa Galadima Manajan wannan Ofis mai kula da shi a shekara ta 2008. (Taskar Suleiman Ginsau)

"AIKIN GALADIMA A KAMFANIN MAI NA NNPC"

Dangane da irin gagarumar gudun mawa da jajircewar sane tasa, daga bisani aka yi masa canjin aiki zuwa Kamfanin NNPC a shekara ta 2012 lokacin da Kamfanin na NNPC ya nemi Kamfanin Total da ya basu shi don ya taimaka wajen canja akalar tafiyadda kamfanin NNPC Retail yadda zai yi daidai da sauran manyan kamfanonin mai na kasuwanci irin su TOTAL.

A yayin zamansa a Kamfanin NNPC na kasa ya samar da ci gaba ta fuskar samar da kudaden shiga masu tarin yawa, ya samu nasarar bude kananan gidajen Mai shiryawa tare tabbatar da tsaftace kasafin kudaden Kamfanin, Galadima ya samar da ci gaban Kamfanin NNPC Retail tare da inganta harkokin kasuwanci a matsayin Janar Manaja mai kula da saye da kasuwanci a karkashin NNPC Retail Ltd, a Abuja cikin watan Maris na 2012.

Haka kuma Kamfanin NNPC ya sake ba shi mukami Janar Manaja mai kula da tsare-tsare da dabarun aiki cikin watan Maris na 2013 a dai karkashin NNPC Retail Ltd.

"A JIYE AIKIN GALADIMA"

Alhamdulillah mai Girma Galadima ya yi aikinsa cikin koshin lafiya tare rikon amana da gaskiya wanda hakan ya bashi damar ajiye aikinsa cikin walwala da jindadin, Galadima ya ajiye aiki don kashin kansa a shekara ta 2014, inda ya kafa Kamfaninsa mai suna ENCEE BUSINESS SERVICES, wanda yake gudanar da shawarwari da horo kan yadda za'a bunkasa harkokin kasuwanci Mai da Iskar Gas...

Galadima yana da matan Aure guda biyu da 'ya'ya Goma... Ina mai addu'a agareshi Allah ya tayashi riko, Allah ya daukaka wannan Masarauta ta Hadejia.

Tsarawa
ISMAILA A SABO


Mai Nazari
SULEIMAN GINSAU
Association Of Nigerian Authors (ANA)

Monday, October 3, 2016

TSARIN ZAMAN JAMA'A DA TATTALIN ARZIKI A KASAR HADEJIYA KAFIN ZUWAN TURAWAN MULKIN MALLAKA. (Kashi na 1). Daga Suleiman Ginsau...









Kasar Hadejiya tana da kabilu daban daban, amma duk da haka wannan masarauta a cure take a waje daya. Addinin Musulunci shi ne ya dada hada su da kuma harshen Hausa wadda suke magana da shi a matsayin harshen kasa. Babu wata tababa cewa Addinin Musulunci shine Addinin da mafi yawan jama'a suke bi a wannan masarautar ta Hadejiya. Ka'idoji da dokoki da hukunce-hukuncen Musulunci su ne suke tafiyar da rayuwa da ayyukan mutanen wannan kasa. Addinin Musulunci ya hada kan jama'a kuma ya samar da hanya madaidaiciya ta zaman al-umma. Ta hakane Musulmi masu rinjaye da wadanda ba Musulmi ba marasa rinjaye mazauna kasar Hadejiya kafin mulkin mallaka suna ganin sarkin Hadejiya nada mutukar kima kuma shugaba ne babba duk da yake suna da hakimai da dagatai wadda suke jagorancinsu, Mutanen Hadejiya sukan hadu a kowace shekara su gudanar da bukukuwan Sallah karama da Sallah babba a Hadejiya.

Ta haka al'ummar Hadejiya take cudanya da juna cikin walwala, farin cikin, nishadi, jindadi da annashuwa da sakin fuska. Kuma bisa dukkan alamu, kabilun da suke zaune a Hadejiya sun shiga juna, za'a taras bisa asali, Bahaushe, Bababbare ne, ko Bamange, ko babade, ko kuma bafulatani. Haka dai kabilun kasar Hadejiya suka sarki juna.

Jama'ar da ba Musulmi ba suna karkashin kariya ta wannan masarauta, amma su kuma suna bayar da jizya. Al'adun Hausawa/Fulani Hadejiya suna da babban tasiri na mutanen Gabas wato al'adun Barebari. Akwai misali da yawa da za a iya bayarwa a kan haka, kauki misalin sunayen wasu mukaman sarautu kamar Zangoma da Bulama da Kacallah da Maina (dan Sarki) duka daga wajen Barebari a ka samo su.

Hatta ma bikin Sallar maulidi ana gudanar da shi ne dai-dai yadda Barebari suke yi. Ashe ke nan al'adun Barebari sun yi tasiri. (Sulaiman Ginsau )
Kari a kan wadanan kyawawan huldodi na mutanen Hadejiya a tsakanin junansu, tsarin da masarautar ta bi wajen tafiyar da al'amuranta na mulki ya dada kara wannan dankon zuminci. Tun daga farkon kafuwar daular, Sarkin Hadejiya Malam Sambo ya dora kowace kabila daga cikin kabilun kasar a kan wani mukami na sarauta. Wannan tsari da aka ci gaba da aiwatar da shi, ya sanya jama'ar kasar sun zauna a dunkule tamkar tsintsiya domin kowace kabila ta san tana da wakilci a majalissar wannan masarauta.


Ta fuskar tattalin arzikin kasa kuwa, Hadejiya tana da yalwataccen arziki tare da sana'o'i da masana'antu iri-iri, duk da yake harkokin noma sunfi daukar kaso mai yawa. Magidanci shi ne tushen arziki a tsarin zaman jama'a tare da iyalansa a matysayin masu taimakawa. Talakawa sun tsayu sosai wajen yin noma na lokacin damina da noman fadamu a lokacin rani, sannan kuma kamun kifi da kiwo sun zama ruwan dare a tsakanin mazauna kasar Hadejiya. Amfanin gonar da aka fi nomawa sun hada da:-
1. Gero
2. Dawa
3. Shinkafa
4. Wake
5. Masara
6. Gyada
7. Auduga
8. Alkama
9. Ridi da Kankana
10. Rake da sauran kayan lambu kamarsu Timatir da Tatttasai da Taruhu da Rake da sauran kayan lanbu ana noma su ne ta hanyar noman fadama a lokacin rani. Kasar Hadejiya, kamar sauran kasashen wannan nahiya, tana da kyakkyawar kasar noma Gero da Kiwon Dabbobi. Har wa yau kuma wannan yanayin wuri ne mai albarka ya ba da damar aiwatar da wasu sana'o'I kamar su Rini da Saka da Kira da Ginin Tukwane da Jima da Dukanci da Gini da sauransu.


A bangaren saka kuwa kauyen Bangelu wanda yake tsakanin Auyo da Hadejiya ya shahara sosai wajen saka da dinka Rigar Bullamai tare da sauran Rigunan Saki Fari masu inganci. Haka kuma kauyen Hadejia ya yayi suna a sana'ar Rini. Mutanen Hadejiya da suke zaune a daura da kogin Hadejiya sunyi fice a sana'ar Su ta kamun kifi. Haka kuma dajin Hadejiya cike yake da kudan zuma inda ake samun zuma mai tarin yawa. Diban zuma ya zama wata sana'a mai riba ga jama'ar kasar Hadejiya musamman yadda take tallafawa wajen warware matsalolin rayuwar yau da kullum.

Bugu da kari mutanen Hadejiya kamar sauran wurare, sukan sayar da amfanin gona wanda ya yi rara, ta haka suka shiga hada-hadar kasuwancin amfanin gona daga cikin hanyoyin da suka kara habaka Tattalin Arzikin Kasar Hadejiya kafin zuwan turawan mulkin mallaka. Ta wannan hanya masarautar Hadejiya ta zama wata cibiya kuma muhimmiyar mahada ta cinikin kayan amfanin yau da kullum a gabacin kasar Hausa a karni na sha tara (K19). Masarautar ta yi fice wajen fitar da kayayyakin abinci kamar Alkama da Kifi zuwa Kano da wasu wurare, ita kuma sai ta sayo Goro da makamancin abubuwan da masarautar take da bukata. Kamar yadda aka fada a baya, mutanen Hadejiya na kasuwancin Rigunan Saki ko Rigunan Fari da Zuma da Kiraga wato (Fatu) da Shanu, su kuma su sayo Gishiri da Dawakai da Kanwa. Ana kuma jin cewa Hadejiya ta zama wata hanya ta fatauci na fataken da suke ratso Sahara zuwa Kano ta yamma da kuma Barebari da Larabawan Fezzan da Azbinawa da Buzaye daga gabas da kuma yamma. Wadannan fataken sukan hadu a kasuwar Hadejiya su gudanar da harkokin cinikayyarsu na kayayyaki kamar Rigunan kano da kanwa da Shanu da Bayi da kayan Yaji (Sulaiman Ginsau).

A wannan lokacin da ake Magana, a Hadejiya akwai manyan kasuwanni guda biyu (2) daya kasuwar an yi ta a wajen ganuwa, an kakkafa rumfunan da kuma masaukai na baki wadanda aka yi don samar da wuraran zama da jin dadin fatake da sauran yan kasuwa. A cikin ganuwa ta birnin Hadejiya akwai wata kasuwa wadda take kula da bukatun mazauna birnin Hadejiya da makwabtanta. Wannan ya nuna cewa bayan kasancewar Hadejiya cibiyar mulkin da ayyukan jin dadi jama'a, haka kuma tana matsayin ingantacciyar cibiya ta kasuwanci. Wannan kasuwa tana karkashin kulawar Zangoma wato Sarkin kasuwa. Zangoma shi ne yake karbar dukkan haraji na wannan kasuwa tare da masu taimka masa.
A dunkule, wannan yayi bayanin Hadejiya a matsayin masarauta ta mulkin jihadi da kuma fito da tsarin zaman jama'arta da tattalin arzikinta kafin mulkin mallaka na turawan ingilashi a kan daular Usmaniyya ta Sakkwato.

An kuma nuna cewa a fanning Siya sa, Hadejiya gari ne na 'yan Boko da 'yan siya sa masu yawan gaske kuma Hadejiya garine na kasuwanci wadda hakan ya sa mutane suna zuwa siyan kayayyaki daga gurare daban-daban, sannan masarautace mai karfi a tsakanin masarautun da suke gabacin kasar Hausa, musamman yadda take tsoma baki a harkokin cikin gida na makwabtan ta.

Haka kuma nayi wai-waye ta fuskar tsaro ya bayyana cewa Hadejiya kasace jaruma kuma karshen karni na sha tara (K19) sai ta zama kasa mai kyakkawar huldar dangantaka da zama na lumana da abokan taka da sauran masarautu. (Sulaiman Ginsau)

Muhadu a kashi na biyu 2