content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!: 2017

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, September 24, 2017

TAURARINMU..... MARIGAYI INJINIYA IBRAHIM BAYI.

HADEJIA A YAU!


Jama'a barkanmu da wannan lokaci, da fatan kuna lafiya. Ga kadan daga Tarihin Rayuwar Marigayi Injiniya Ibrahim Bayi, wadda shima yana cikin Sahun mutanen da muka kirasu da suna........ "TAURARINMU"

An haifi Engineer Ibrahim Bayi a garin Hadejia Mahaifinsa shine Mallam Muhammadu Sarkin Yarin Hadejia, ya fara karatu a Makarantar Elementary ta Hadejia Wadda ake kira Abdulkadir Primary a yanzu a shekarar 1939 zuwa 1942. Sannan ya tafi makarantar Middle dake kano a shekarar 1942 zuwa 1945. Daga nan Ibrahim Bayi ya tafi makarantar Barewa College a shekara ta 1945 inda ya gama a shekarar 1948. Bayan ya dawo Hadejia ya tabawa N. A. Aiki na 'yan shekaru a ofishin Wakilin Sana'a sai ya koma Kaduna inda anan ne ya samu damar zuwa makarantar Brighton College of Technology wadda yanzu ake kiranta University of Sussex ta Brighton a shekarar 1958 zuwa 1962, Inda ya samu shaidar takardar Diploma in mechanical engineering.

Engineer Ibrahim Bayi yayi Ayyuka a wurare daban daban a fadin Nigeria, kuma ya zama Bubban Engineer a shekarar 1966. An zabe shi member na cibiyar Harkokin Masana'antu ta Birtaniya (MI MECH E.) Yayi aiki a Kamfanin Harkokin tsaro a shekarar 1968, inda ya zama Janar Manaja a Shekarar 1972. A shekarar 1976 zuwa 1980 ya zama shugaban hukumar bada ruwan sha ta jihar Kano (WRECA). Wannan Bawan Allah ya samarwa mutane Ayyuka daban daban, sannan ta dalilinsa Hadejia ta samu ma'aikatun Gwamnatin Tarayya kamar su Nepa, Nitel, Post Office da sauransu. 

Engineer Ibrahim Bayi ya samu lambar girma ta hannun gwamnatin Koriya ta Kudu a shekarar 1982, yayi ritaya daga aiki a shekarar 1985. Sannan ya zama shugaban kwamatin gudanarwa a kwalejin kimiyya da fasaha dake Mubi tsakanin 1986 zuwa 1993. Ya zama member a hukumar Jigawa resources Development Agency 1995 zuwa 1999.  Engineer Ibrahim Bayi ya rasu a gidansa dake Kaduna Ranar Laraba 9/July/2014, ya rasu yana da shekara 84 a Duniya. Ya bar matar Aure da 'ya'ya goma (10) da Jikoki Ashirin da biyar (25). Allah ya gafarta masa da rahma tare da Iyayen mu.

Sunday, August 6, 2017

AN RATAYAWA SARKIN KANO SUNUSI LAMBAR GIRMA TA K.B.E.

HADEJIA A YAU!

AN RATAYA WA SARKIN KANO SUNUSI LAMBAR GIRMA TA K.B.E.





A cikin watan Satumba/1958, bubban Razdan na Kano Sir. Gawain Bell ya ratayawa Sarkin Kano Muhammadu Sunusi lambar Girma ta K.B.E. anyi gagarumin Hwan Daba inda aka kewaya gari daga nan aka nufo Ƙofar Fada inda anan ne aka ratayawa Sarki wannan lamba. Mutanen da sukayi kallon Dabar sun kwatanta ta da Dabar da aka yiwa Sarauniya. Sarakunan Ƙasar nan da yawa da manyan Ma'aikatan Gwamnati ne suka halarci wannan taro, a cikinsu harda Firimiyan Jihar Arewa Sir. Ahmadu Bello da Ministocinsa, har ma da Mukaddashin firayim Minista Sir. Abubakar Tafawa Ɓalewa.

Kimanin mutane Dubu Talatin (30,000) ne suka halarci taron shagalin Baiwa Sarki Sunusi wannan lambar Girma, ciki da wajen Jihar Arewa, abin sha'awa Sarkin Musulmi Sir. Abubakar da ya halarci taron ance rabonsa da Kano shekara 16 kenan. Firayim Minista bai samu zuwa ba amma Muhammadu Ribadu ya wakilce shi. Cikin manyan Baƙi harda Chif Jojin Sudan wadda Gwamnatin Arewa ta gayyato domin binciken Al'amuran Shari'ah a wannan Jiha, da kuma Wakilin Amurka a Nijeriya. Bayan an kimtsa duk manyan Baƙi sun zauna a Cikin Ƙwatattun Rumfuna sai Gwamnan Arewa ya nufo Ƙofar Mata inda aka je aka taryoshi akan Dawaki, Sarkin Kano da Hakimai da mahaya Dawaki duk aka tafi taryen Gwamna. Bayan sun gaisa da Sarki shima Gwamna sai ya hau Doki aka nufi ƙofar Kudu inda ake Shagalin bikin, ‘yan Doka masu Badujala ne suka share musu hanya suna tafe suna kiɗa da busa, Gwamna na tafe tare da Muƙaddashin Razdan na Kano Mr. melinctock. Sarki kuma na biye dasu da Dogarai da ‘yan Sulke da ‘yan Kwalkwali har zuwa ƙofar Kudu. 

Sarkin Musulmi Abubakar tare da Sarkin Gwandu sune suka kai Sarki Sunusi Rumfar da za’a rataya masa Lambar Girman, daga nan sai Razdan ya miƙe ya karanta saƙon Sarauniya na bayar da Lambar, sannan sai Gwamna ya miƙe ya Ratayawa Sarkin Kano Sunusi lambar, sai wuri ya kaure da Tafi da shewa da kiɗe kiɗe da Bushe bushe don murna.


WANNAN DARAJA TA KOWA CE.
Sarkin Kano Sunusi ya miƙe yayi jawabi inda ya fara da godewa Allah (swa), sannan yace “Ina godiya ga Allah wadda da ikonsa ne wannan abu ya kasance a rana irin ta yau, sannan ina ƙara godiya ga Mai Martaba Sarauniya saboda wannan Daraja da ta bani, tare da shaidar Amincewa a rataya min a gaban Jama’a. Wannan Daraja ta shafi kowa ba ƙasar Kano kawai ba, harda duk Jihar Arewa. Na tabbatar da wannan shine lokaci na biyu da aka bada irin wannan Lambar girma a Jihar Arewa, mu duka munyi farin ciki da Alfahari a lokacin da Sarkin Ingila King George na 6 ya baiwa Sarkin Musulmi irin wannan lambar, to ina Alfahari da cewa nine na Biyu da aka baiwa wannan lamba, nayi Alƙawari zanyi matuƙar ƙoƙarin da zan iya in nuna na dace da wannan lamba da aka bani.




ZAMA MASU ZUMUNCI DA INGILA.
Da Sarkin Kano Sir. Muhammadu Sunusi ya Juyo wajen Maganar Samun Mulkin Kai sai yace, "Yau saura watanni goma sha takwas 18, muke zaton samun cikakken mulkin kai na Nijeriya. Mun lura da irin wahalce wahalcen dake gabanmu, amma duk lokacin da na hangi waɗannan wahalce wahalce nakan ji daɗi idan na tuna ƙasar nan zata zama ɗaya daga cikin ƙasashen da suke haɗa kai da Ingila. Da taimakonsu da kuma Jagoransa, in Allah ya yarda ƙasarmu zatayi ta ci gaba da Arziƙi."

Bayan Sarkin Kano Sunusi ya gama Jawabi sai aka Sallami kowa, duka manyan Baƙi suka tafi masauƙi. Da daddare kuwa Jam'iyyar NPC ta shirya wata ƙasaitacciyar rawa a Randabu Hotel saboda murnar bayar da lamba girma ga Sarkin Kano Muhammadu Sunusi. Alhaji Mai-wada M.H.A. shine ya shugabanci bikin Rawar.

MADOGARA...
Gaskiya Ta fi Kobo
EAP/485-11-397

Tuesday, June 27, 2017

HADEJIA TOWN ASSESMENT REPORT BY H.N. BRICE SMITH, A.D.O. DECEMBER 1916.

HADEJIA A YAU!

   
1. No previous Assesment Report of Hadejia Town has been written, the only records available are those contained in Mr. A.C.G. Hastings General Assesment Repotr of the Hadejia Emirate compiledin March 1910.

2. The town is situated almost in the centre of the Emirate, and is surrounded by the Districts of Teffida Mabudee and Sarkin Dawaki.

3. The river Hadejiaa flowing east, lies as its nearest point a little more than a quarter of a mile from the south west gate. It begins to flow in the middle of June and continues until the end of November. During the rest of the year water is obtainable from pools or by digging in the river bed.

4. There are in addition 83 wells in the town itself, There is therefore an ample water supply available all the year round.

5. The Town had three Walls:-
(1) Dating from pre Fulani times, had four gates. It can be traced at the present  day by certain pits, Maikilabo on the west near the present Alkali's house, Attefi on the south near Gidan Sarkin Busa, and Dellah on the east near the house of the present Galladima. It was about one mile in circumference.
(2) Built by the fulani Sarki Sambo of Hadejia is difficult to trace except on the east where it follows approximately the eastern limit of houses, and on the west where it passes a "Chediya" tree east of the present market. it had five gates. Its perimeter was 2 miles 170 yards approximately. 
(3) Also built by Sarki Sambo is the present wall but when first built it did not extend on the east side of the town beyond the previous wall. the Habe settlement of Fantai remained outside it on the east. This wall was finally extended to its present size by Sarki Haruna, father of Sarki Muhammadu, who fell in the fighting with the Administration in 1906.

Haruna enclosed a large open space on the east to harbour fugitive villagers in case of war. There are five (5) gates. Its perimeter is now 4 miles 135 yards.
(4) The wall was divided up into section, for the repair of which certain villagers used to be responsible. The various gates are still in care of certain of the Sarakuna.
1. The Kofar Arewa.............. Sarkin Arewa
2. Kofar Gabas.................... Madawaki
3. Kofar Kudu.................... Teffida
4. Kofar Kogi................... Galadima
5.  Kofar Yamma.............. Sarkin Dawaki.

(5) It has been necessary frequently in the past to build temporary walls outside on the South side to prevent flood water from entering the town.

(6) For Three (3) months during the Bazara season of the present year 1916 a mirage (Hausa 'Kauwalwarniya') was visible on the open space between the eastern side of the town and the wall. A similar phenomenon was last seen 32 years ago when the Shehu of Bornu capture the town of Kadera in Adiyani District or Chiroma District. It was expected to portend some exceptional event and was followed by one of the heaviest rain falls within memory.

(7) The town is almost entirely composed of flat roof-ed mud houses and is well kept and clean.

(8) The market is situated inside the town neaar the west gate. The booth are of mud with a few grass (Rumfuna). It is held daily, but the Chief market day is Sunday. The slaughter ground has recently been removed from the market to a spot on the west side, outside the town walls.

(9) Sanitation is on the whole good, the town is noticably free from odours.

(10) Hadejia possesses no Historical document, Authentic History dates only from the founding of the Fulani dynasty early in the 19th Century. It has been recorded in Captain J.M. Fremanle's History of Katagum and in Mr. A.C.G. Hasting's assesment report on Hadejia Emirate written in 1910.

(11) Additional information has been obtained for this report from the following authorities;-
(a) The Galadiman Hadejia-- Usuman
(b) Moman Jekada (one of the Emir Abdulkadir's retinue)
(c) An aged man named Mallam, one of the few surviving descendants of the Habes of pre-fulani times.

The town was founded by a hunter named HADE, a Barebari from Machina (Bornu). Hadejia wandered south hunting, and finding a favourable hunting ground, hung up his quiver on certain 'Tsamiya' tree under which he was resting. His Dog wandered off and his master noticed on its return that it had found water to quench its thirst. He followed the dog which led him to a river. He thereupon returned to Machina and reported to his family that he had found a suitable place for a house, and subsequently  returned with them to the spot. This place proved to be in the country of Auyo, a flourishing Habe town at the time which had been founded about 1,400 A.D. He took to wife a lame woman of the Auyokawa, who lived in a small hamlet nearby. A town sprang up and he was made first Sarki of Hadejia. He was followed by a series of 32 Habe Chiefs, of whom only the names of three are known today, i.e. BAUDE, MUSA And ABUBAKAR. During the reign of Abubakar of Hadejia and Jibrin of Auyo, the fulani arrived from Gobir (via Massina) seeking grazing grounds..................Hadejia A yau.         continued.....  

Wednesday, May 24, 2017

HADEJIA IN THE YEAR 1856.

HADEJIA A YAU!





 TRAVEL AND DISCOVERIES OF NORTH AND CENTRAL AFRICA... BY HENRICH BARTH.
(PAGE 236)

With regard to the Empire of Sokoto, there happened at this time a catastrophe which while it was an unmistakable proof of the devility of that vast agglomeration of provinces, proved at the same time extremely favourable to Bornu; For on the first day of August the news arrived that Buwari or Bukhari the exile Governor of Hadejia, who had conquered the town and killed his Brother Ahmadu, had thrown back with great loss, an immense army sent against him by Aliyu, the Emperor of Sokoto, under the command of his prime minister Abdu Gedado, and composed of the forces of the provinces of Kano, Bauchi,Katagum, Marmar and Buberu, when several hundreds were said to have perish in the Komadugu, or the great fiumara of Bornu.

TRAVEL AND DISCOVERY IN NORTH AND CENTRAL AFRICA.....  By Heinrich Barth 1856. Chapter XXVI. Page 196.

Hadeja, a  large  town surrounded with a beautiful  and very strong double clay wall, and well  inhabited, the  courtyards being  inclosed  with  clay  walls,  but containing only reed huts.

The inhabitants employ  themselves exclusively in warlike expe¬ditions, and have no industry; but nevertheless there are  still to be seen here a few dyeing-pots, marking the eastern limit  of  this branch of industry.  On the south side of the town is a kogi, or komadugu,  with a  stream of running water in the  rainy  season,but  with only stagnant  pools in summer, along which a little wheat is  cultivated.  It is generally called Wani.

  6th. Garu-n-ghabbes,  a middle-sized  walled  town,  the  first place of Bornu, on this side 3 with a good deal of cultivation around. Though without importance in other respects, it is so in  an his¬torical point of view ; for this place being identical with the town Biram ta ghabbes, mentioned  above, is  regarded as  the oldest place of the seven original settlements  of the Hausa nation.

Thursday, May 11, 2017

BUKHARI OF HADEJIA... (By Henry Barth)

HADEJIA A YAU!

Travel and discovery in North and central  Africa. By Henry  Barth.......... 

March 18.] BENZARI— BUKHARI OF HADEJA. 323 

Any protection in the neighbourhood of some villages. After we had passed the empty market-place of the little walled town Kabbori, the surface of the ground had a very peculiar look, being covered entirely with colocynths, which were just in maturity. About a mile and a half further on we took up our quarters in Benzari, a town belonging to the province of Mashena, or Maseena, and were well received and hospitably treated by the Ghaladima. The town is separated into two parts by a spacious opening, wherein is the principal well which supplies almost the whole population, but its depth is considerable, being more than twenty fathoms. Here we filled our water-skin the next morning before we set out. 



Tuesday ', March 18. — Scarcely had we left Benzari behind us when my ears were struck by the distant sound of drums and singing, and I learnt on inquiry that it was Bukhari, or, as the Bornu people call him, Buwari, the deposed governor of Hadeja and the brother of Ahmedu, the present ruler of that town. Bokhari's name was then new, not only to me, but even to the natives of the neighbouring provinces. He had been governor of Hadeja, but being a clever and restless man he, or rather his jealous brother,  excited the suspicion of his liege lord 'Aliyu, the ruler of Sokoto, who had deposed him and given the govern-ment to his brother Ahmedu,where upon Bokhari had nothing else to do but to throw himself upon the hospitality and protection of the Bornu people, who received him with open arms, the governor of Mashena, with the sanction of his liege lord the sheikh of Bornu, assigning to him a neighbouring place, Yerimari, for his residence.
This is an incident of very frequent occurrence in these loosely connected empires; but it is particularly so with the Fulbe, among whom one brother often cherishes the most inveterate hatred against another. Exactly the same thing we have seen already in Katsena. Bokhari having remained some time quietly in this place, strengthening his party and assisted underhand with arms and men by the vizier of Bornu, had just now set out to try his fortune against his brother, and was beating the drums in order to collect as many people as possible. Predatory incursions are nothing new in these quarters, where several  provinces and entirely distinct empires have a common frontier; but this, as the event proved, was rather a memorable campaign fortfie whole of this part of Negroland, and was to become "the beginning of sorrows" for all the country around. For Bokhari having taken the strongtrong town of Hadeja, and killed his brother, was not only able to defend himself in his new position, vanquishing all the armies sent against him, and amongst them the whole military force of the empire of Sokoto, which was led on by the vizier in person, 'Abdu the son of Gedado, Clapperton's old friend, but spread terror and devastation to thevery gates of Kano. Indeed, on my second journey through these regions, I shall have the sad duty of describing the state of misery into which districts, which on my former visit I had found flourishing and populous, had been reduced by this warlike chieftain, who instead of founding a strong kingdom and showing himself a great prince, chose rather, like most of his countrymen, to  his power on the destruction. eir 'of 

324. TRAVELS OF AFRICA. [185]  
and devastation of the country around him, and to make himsetf a slave- dealer on a grand scale. Tens of thousands of unfortunate people, pagans as well as Mohammedans, unprotected in their wellbeing by their lazy and effeminate rulers, have from the hands of Bokhari passed into those of the slave-dealer, and have been carried away from their native home into distant regions. Kept in alarm by the drumming, and making some not very tranquilling reflections on the weakness of our little band, which consisted three men and a boy, in the turbulent state of the country through which we were passing, we continued silently on, while the character of the landscape had nothing peculiarly adapted to cheer the mind. 
Cultivation beginning to cease, nothing was to be seen but an immense level tract of country covered with the monotonous Asclepias gigantea with only a single poor Balanites now and then. But the scene became more animated as we approached Chifowa, (Shafowa) a considerable town sur-rounded by a low earthen wall, which I was greatly astonished to hear belonged still to the territory of Gummel, and was also assigned to Bokhari during his exile. The boundary between the provinces must run here in a very waving line. 

All that I observed here testified that the Hausa population still greatly  predominated; and as we had to turn close round the place on the north side, where the ground rose, we had a fine view over the whole interior of the town. It presented a very animated spectacle; and a large number of horsemen were assembled here, evidently in connection with the enterprise of Bokhari, while men and women were busy carrying water into the town from a considerable distance. Of  cultivation, however, very few traces appeared ; but a good many cattle and sheep, and even some camels, were seen grazing about. In Kase-Itiwa also, the next town, we were complimented with the usual Hausa salute. Having then passed through a monotonous tract of country covered with tall reed-grass and with the Asclepias, we reached the town of Yelkazl at half-past nine o'clock in the morning. Here the governor of the province of Mashena, who generally has his residence in the town of the same name, was staying at present, apparently on account of the expedition of Bokhari, which he was assisting under-hand ; and I accordingly had to pay him my compliments, as my horseman, who was a servant of Dan-Tanoma, could not well conduct me any further. We therefore entered the town by the north gate, and found people very busy repairing the fortification, consisting of two walls and three ditches of considerable depth, two of which ran outside round the outer wall, while the third was enclosed between the two walls. 

Having presented ourselves at the residence of the governor, which was situated in the middle of the town, and consisted altogether of reed-work, we obtained good quarters, with a spacious and cool shed, which was the only thing we wanted ; for being anxious not to lose any more time, I had resolved to start again in the afternoon. In order, therefore, to obtain a guide as soon as possible, I went to pay my compliments to the governor, whose name was Mohammed. After a little delay.

March 1 8.] THE  GOVERNOR OF MASHENA.—TAGANAMA. 32

Sunday, February 12, 2017

TARIHIN ƊAN HAUSA (Sir Hanns Vischer)

HADEJIA A YAU!


An haifi Ɗan Hausa a cikin shekarar 1876, bai fara aiki a ko ina ba sai a Nigeria a cikin shekarar 1903. ya fara aiki a matsayin mataimakin Razdan, kuma sunansa shine Sir. Hanns Vischer, ya fara zuwa Ƙasar nan akan aikin Mishan ne. ya fara zuwa ƙasar nan ne tare da Dr. W.R.  Miller da Sarkin Hausa Reb. G.P. Bargery, farkon samun aikinsa an ajiyeshi a waɗansu wurare harma ya taɓa zama a Barno. yana can Barno ne yayi tafiya da Ayarin Raƙuma daga Tarabulus zuwa Barno ta hanyar Marzuk. har ya rubuta littafi akan tafiyarsa, wadda ya sakawa suna ƙetarar Sahara. yayi wannan tafiya tare da wani yaronsa da ake ƙira Sa'id. shi Sa'id ya daɗe yana Masinja sai a shekarar 1945 ya rasu, duk waɗanda sukayi makaranta a Nasarawa ta kano sun sanshi.

Cikin shekarar 1908, Ɗan Hausa ya zama gwamnan makaranta har yaje ƙasar Sudan don ya koyo yadda za'a shirya Al'amarin Ilmi anan. A shekarar 1910 ya kafa makarantar Turawa a Nasarawa dake Kano, yara da samarin da aka buɗe makarantar dasu bayan shekara uku kuma sai su fita suje suyi koyarwa a makarantu na ƙasashensu, kamar su Katsina, Sokoto, Barno, Bidda da Zariya. Wannan makaranta ta Ɗan Hausa tana nan a kusa da ofishin Razdan na Kano kuma har yanzu wannan gida yana nan. Cikin shekarar 1915 ya shiga aikin soja har ya zama laftanal aka gama shi da masu kula da shirin labaran yaƙi, ana nan har ya zama kyaftin har dai ya kai matsayin Manjo. Cikin watan Yuli 1917 Ɗan Hausa ya koma Ingila sakamakon Jinya da ta dameshi, amma dukda haka bayan ya koma Ingila yaci gaba da Taimakon ƙasar nan ta hanyar Ilmi. 
Ɗan Hausa yakan riƙa bada labarin zamansa a ƙasar nan har yakan riƙa bada labarin wani Masinjan Razdan na ƙasar nan Mr. George Tomlinson, lokacin da Masinjan zai je Hajji sai da ya isa Bahar Muhid aka ce ya makara, da zai koma gida ya kewayo ya biyo ta Bahar Rum. har ya isa Birnin Southampton inda Ɗan Hausa yake aiki. anan ya zauna a tashar Jirgin Ruwa tare da sauran fasinja, amma da 'yan Gadin sukaga irin siffarsa sai suka ƙi yarda dashi suka kai shi wurin Ɗan Hausa. Shi da ganin mutumin ya san Bahaushe ne amma Ɗan Hausa bai nuna masa ya iya Hausa ba, sai ya faɗa shi da tambaya da turanci, Bahaushen nan tsoro ya kama shi, amma da yaji Ɗan Hausa ya masa magana da Hausa sai yayi ta kuka don murna. ya sa aka bashi masauƙi mai kyau kuma ya gamashi da Takarda cewa mutumin nan abokin aikinsa ne na Africa. kaga bai taɓa sanin mutumin ba amma saboda yana ƙaunar mutanen  Africa yayi masa wannan Darajar. Cikin 1917 aka kai Ɗan Hausa ofis ɗin wakilin Ingila dake Spain ya zauna acan har aka gama yaƙi.
A shekarar 1923 ya zama sakataren wata jam'iyya mai lura da yadda za'a shirya zancen ilmi a ƙasashen da suke ƙarƙashin mulkin Ingila, kafin ya huta a wannan aiki ne ya samu bubbar lambar Girma ya zama ''Knight'' yana cikin waɗanda suka kafa jam'iyya mai lura da zancen harsuna na Africa watau ''Institute of African Languages and cultures''
Mallam Bello Kagara yace.... 

Haƙiƙa ya cancanci ace dashi Ɗan Hausa, don dabarar sa da yayi nufin bude makarantu anan Nijeriya ta Arewa sai yaje Sakkwato a hankali ya fara da can ya ɗauko ta daga tushe. Bayan haka kuma yaga babu inda ya kamata ya kafa makarantar sai tsakiyar jama'a watau Birnin Kano, sai yaje Nasarawa gabas da kano ya bude ta". Da fari bai ɗauki kowa ba sai 'ya'yan sarakuna, da Hakimai, da Alkalai, da shaihunnan maluma. 

Akwai manyan Sarakuna daga cikin Almajiran sa, kamar sarkin Gwandu da Sarkin Zazzau, da Lamidon Adamawa Mustapha da Sarkin Yawuri, Hakimai kuwa Allah yayi yawa dasu! Sunan Ɗan Hausa har abada bashi ɓata anan ƙasar musamman a ƙasar Kano.  


Malam Bello Kagara yace... "babu abinda yake ban mamaki kamar zamanmu dashi a Nasarawa, ga Almajiran sa cikin Aji da Amawali da Alkyabbu, dasu da malamai sun zama bubba da hula yaro da hula, ga Dawakai da zagage a ƙofar makaranta duk na Almajiran sa ne suna jira a tashi su hau. Amma duk da haka Ɗan Hausa ya ƙyale mu, kowannen mu in safiya tayi zamuyi shara tun daga ciki har waje, ga Barorinmu na kallo basu da ikon su karbe mu. Mu ratsa Kano har Dala mu ɗauko fid da sartse a kai, alhali kuwa ga Dawaki da zagage da Alkyabbu sun riƙe a ƙofar makaranta".
A cikin 1913, yaga malamai sun samu sai ya fara bude makarantu a manyan Alƙaryu don a watsa Ilmi a ko ina, dubi yanzu yadda abu ya tabbata. Amma kam kada ka tona wahalar da Turawan farko suka sha kafin Ilmin Boko ya tabbata..... 

MADOGARA.... 
Gaskiya tafi kobo ta 175.
Sir. Hanns Wikipedia 
Eap.bl.uk. 

Sunday, January 15, 2017

SARKIN MUSULMI SIR. ABUBAKAR III.

HADEJIA A YAU!


SARKIN MUSULMI ABUBAKAR. 
Cikin 1902, ana kamar badi Turawa zasu zo Sokoto anka haifeni a wani gari wai shi Dange. Tun ina dan shekara Bakwai (7) Marigayi Sarkin Musulmi Hassan ya riƙe ni, da na dan yi wayo na isa fara karatu, da yake Sarkin Musulmi Malami ne bai kai ni kowace makaranta ba, sai ya tsareni nan gaba nai shina koya min karatu. Shina kuma kula dani da hana ni yawan Shedana irin ta yara. 

Lokacin da Sarkin Musulmi Hassan ke Mallamin Uban Kasar Dange (Hakimin Dange),  da na fara ido wajen Karatu sai nayi ta taimako nai wajen Aikinga. Muna nan haka cikin Shekarar 1923, Sarkin Musulmi Hassan ya sami Sarautar Sarkin Bauran Dange. Da ya sami wannan Sarautar ni kuma sai ya maishe ni matsayi nai na zama ni am Mallami nai. (Malamin Hakimi). 

Muna nan haka har cikin shekarar 1931, Allah ya nufa Sarkin Musulmi Hassan ya zama Sarkin Musulmi. Da anka natsa sai ya dauko ni daga Dange ya maida ni Sokoto ya nada ni Sardauna, na zama daya daga cikin mataimaka nai ga harkokin kasa.  A cikin Birni kuma ya sa in rinka kula da dukkan wurare na Aiki, kamar su Gidan Yari,  Gidan Ayyuka, likitocin Shanu, Gandun Daji, Dagarawa da dai Sauransu. A wannan lokacin har Kaduna nazo koyon Aikin 'yan Doka dan in samu sanin hanyar taimakonsu. In ko na fita Rangadi in ka jini a wajen wanga Uban kasa yau gobe sai ka jini a wajen wancan, musamman lokacin Haraji ko Jangali. Wani lokaci nakanyi wata biyar ko shida ban leko cikin Birni ba. 

Muna nan haka sai anka yi mani  Uban Kasar Talatar Mafara, nayi watanni hudu (4) ina wagga Sarauta, sai Allah ya yiwa Sarkin Musulmi Hassan rasuwa cikin Shekarar 1938, Allah shi gafarta masa Amin. Bayan rasuwa tai ni kuma Allah ya kawo ni wagga Matsayi. Ina fatan Ubangiji Allah shi taya ni rikawa. 

Sarkin Musulmi Abubakar shine dan Usman,  Usman dan Sarkin Musulmi Mu'azu (wato uban Marigayi Sarkin Musulmi Hassan) Sarkin Musulmi Mu'azu dan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello, Sarkin Musulmi Bello dan Shaihu Usman Dan Hodiyo. Allah shi gafarta musu baki daya Amin. 

Sarkin Musulmi Abubakar bai shiga makarantar Turawa ba amma ya koyi Rubutu da Karatu irin nasu. Sarkin Musulmi Abubakar  shine Sarkin da yafi kowa dadewa a Sarautar Sarkin Musulmi, domin ya shekara Hamsin yana kan Halifar Shehu  Usman Dan Hodiyo. Ya fara Sarauta tun lokacin Turawa,  An nada shi ranar 17/yuni/1938, Razdan na Sokoto  Commander J. Carrow shine ya nada shi. Sarkin Musulmi Abubakar yayi Aiki da Gwamnatoci  Takwas (8), a Nigeria bayan samun 'yancin  Kai.  Bayan zamansa Sarkin Musulmi shine ya Baiwa Ahmadu Bello Sarautarsa ta Sardauna a cikin shekarar 1938. Ya rasu yana da shekaru 85 a Duniya,  ya rasu a cikin shekarar 1988. Allah ya Gafarta masa da rahma tare da Al' ummar Annabi baki daya. 


Madogara....... 
1. Sultan Abubakar lll, Littafin Jean Boyd da Hamzat M. Maishanu.
2. Sultan Muhd. Maccido  in the shadow of his Ancestors,  Littafin Hassana Isma'ila Bichi.
3. Gaskiya ta fi Kobo ta Hudu (4) 1939.