content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Saturday, March 31, 2012

SARKIN HADEJIA BUHARI DA WAZIRIN SOKOTO A KATAGUM (1)

Image Hosted by ImageTitan.com
HADEJIA A YAU! A lokacinda Sarkin Musulmi Aliyu Bubba ya turo Wazirin Sokoto Abdulkadir Gidado Gurin Sarkin Hadejia Buhari, Wazirin Sokoto shine wakilin sarkin Musulmi a yankin Gabas sai ya taho Hadejia daga Kano Amma sai ya wuce Katagum, Ya turo Jakada zuwa Hadejia yana So su Gana da Sarki Buhari.

Buhari yayi tunanin ya tafi shi kadai daga baya sai ya canza shawara kawai ya Tafi Katagum Da Mutanensa. zasu gamu da Wazirin Sokoto a can. Lokacinda suka isa Katagum Sarkin Hadejia Buhari ya tsaya a Kofar Garin Katagum sai ya tura a fadawa Waziri Ya Iso Wazirin Sokoto da Sarkin Katagum suka zo sai sukace Buhari ya Biyosu amma shi kadai tunda Shawara zasuyi.

Sarki Buhari ya bisu Har ya shiga Kofar Garin Katagum. Sai Mawakinsa wato DAN FATIMA ya fara masa waka yana cewa:-

1, Abubakar Garba Mijin Maza,

2, Buhari kai ke da Nutso Kai ke da Hankali.

3, Don Allah yayi ka Uban Jama'a

4, Kuma kai Allah ya baiwa shugabancin Gidan Sambo

5, Ba dan na isa ba, In ka yarda ga Aike ka shiga dashi

6, Fasa Maza Gagara gasa Aiken shine

7, In ka sauka lafiya ka gaida Na Lara Sarkin Auyo

8, Ka gaida Bello Sarkin Dutse

9, Na Sambo sai ka dawo.

Abinda Dan fatima yake Nufi Sarkin Auyo da Sarkin Dutse duk Buhari ya kashe su. Dan haka shima In ya shiga Katagum Lalle Bazai fito ba.

KodaSarki Buhari yaji Wannan Waka ta Dan fatima sai ya juyo da baya, Wazirin sokoto da Sarkin Katagum da suka fahimci Buhari ya juya sai suka Biyoshi da Ihu Su da mutanen Katagum Suna ce masa Kafiri yaki bin Umarnin Sarkin Musulmi. sai da suka biyoshi har Unik Iyakar Hadejia Da Katagum. kuma sun kashe wasu daga mutanen Buhari. koda yazo Unik sai ya yanke Shawarar ya yi sansani a nan ya koma ya yaki Katagum. kuma mutanensa suka koma suka Karkashe Mutanen Katagum karkashin jagorancin Barde Risku. Daga nan Rashin Jituwa Tsakanin Hadejia da Katagum ya Fara har bayan shekara Goma sha biyu bayan Mutuwar Buhari.

(1863). daga nan Aka samu wasa tsakanin Hadejia da Katagum. koda Katagumawa suka juya sai Wazirin Sokoto ya sake Gyyato Mutanen kano suka Hadu da Na Katagum zasuzo su yaki Buhari. da sarki Buhari yaji wannan Labarin sai shi da mutanensa suka bar Hadejia suka tafi Shabawa Iyakar Hadejia da Gumel Sukayi sansani a can.

da Buhari ya bar Hadejia sai Wazirin sokoto ya nada Wansa Ahmadu Sarkin Hadejia. A shekarar (1850). Wanda dama saboda shi suka Takurawa Sarki buhari.

Tuesday, March 27, 2012

TARIHIN SARKIN HADEJIA UMARU DAN BUHARI 1863-1865:

HADEJIA A YAU!

SARKIN HADEJIA UMARU: A SHEKARAR 1863 allah ya yiwa Sarkin Hadejia Buhari rasuwa a Yakinsu da sukayi da Gogaram (bade). Ko da aka dawo Hadejia aka binne shi sai Manyan fadawan Hadejia wadanda akwai Amana tsakaninsu dashi Buhari. Kamar SARKIN AREWA TATA GANA (GINSAU MAI KINA BAWO) DA KUMA SARKIN YAKI JAJI suka jajirce Sai an Nada UMARU DAN BUHARI SARKIN HADEJIA. kuma hakan Akayi!
SARKIN HADEJIA UMARU NA BIYU an nadashi yana da shekara Goma sha Hudu. Kuma manyan fadawan Mahaifinsa sune suke gudanar da Sarautar tunda shi yaro ne. Kuma a zamaninsa Sarkin Damagaram Tanimu ya kawo yaki Hadejia. Kuma yayi sansani a Arewa da Hadejia daga nan har Jigawar Kasim mutanensa ne. saida yayi kwana Arba'in ana yaki amma Hadejiawa basu fasa wasanninsu na dandali ba. Wata rana ana yaki Sai aka harbi dokin Sarkin Arewa! Koda ya mutu sai akaje gida aka dauko wani Dokin aka cire kayan wancan Dokin aka sakawa wanda aka kawo. Tata gana ya koma kan doki, kashe gari ana cikin yaki sai Tata gana ya sauko daga Dokinsa yayi alwala ya koma kan Dokin, to ashe Sarkin Damagaram yana kallon su sai yace Lalle Sarkin Hadejia ya Isa ana yaki ka sauko kayi alwala? Jiya ma an kashe masa Doki amma saida akaje aka dauko wani a gari? Sai Zagin Sarkin Damagaram yace ai ba Sarkin Hadejia bane Yaronsa ne! Sai Sarkin Damagaram Tanimu yace to Ina Sarkin Hadejian? Sai zaginsa yace ai ance yana gida tunda aka fara yakin nan bai taba zuwa ba. Sai sarkin Damagarm yace wa fadawansa Gobe zamu bar Hadejia kar mu tsaya ayi ta kashemu. Saboda Sarkin Hadejia ya raina mu kwananmu Arba'in amma bai taba zuwa anyi yaki dashi ba? Wa yasan me zai mana in ya zo? Amma basu san Sarkin Yaro bane. Washe gari suka juya suka koma Damagaram. Kuma lokacinda sukazo Hadejia Da kaka ne! Anyi girbi Manoma basu gama Tare Amfaninsu ba. Shi yasa suka dade a Hadejia saboda akwai abinci da ruwa a kusa dasu. SARKIN HADEJIA UMARU Mutum ne mai son Nishadi kowane Lokaci yakan fita Bakin kogi ko Gona Domin Debe kewa. Kuma anyi amfani da wannan Damar inda wata rana ya fita sai aka Rufe Masa Kofa. Koda yazo yaga kofa A rufe sai ya juya ya tafi Chamo ya zauna. Aka nada Kanin Mahaifinsa Sarkin Hadejia Wato HARU BUBBA. 1865-1885. Shi kuwa UMARU DAN BUHARI yayi zamansa a Chamo kuma Ya rasu a shekarar 1920. Allah yaji Kansu Ameen.

HADEJIA A YAU.