"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, June 19, 2012

KOFOFIN HADEJIA



HADEJIA A YAU! Wadannan Hoton kofar Gabas ne da Kofar Kudu. An Gina wadannan kofofi ne Tun kafuwar Hadejia kuma haka nan akayi ta gyaransu har zuwa yau. sai dai kash! sakamakon Biris da halin ko in kula ya jefa wadannan kofofi a cikin tsaka mai wuya. kamar kofar Gabas wani yanki daga cikinta tuni ya rushe. Haka Kofar kudu wato Cediyar kyalesu in kaje wucewa idan ba kula kayi ba bazaka san akwai kofa a gurinba. muna kira Ga Karamar hukumar Hadejia da Masarautar Hadejia da a taimaka a gyara wadannan kofofi kamar sauran kofofi 'yan-uwansu. Ganin cewa ba dan ana gyaransu ba da basu kawo yanzu ba. kuma muna kira ga Sarakunan kofofi da su rinka yiwa Karamar Hukuma tuni akai akai domin a gyara wadannan kofofin. Allah ya Daukaka Masarautar Hadejia. Hadejia A yau.

HADEJIA A YAU! An sake sanya dokar awa Ashirin da hudu a Jihar Kaduna Sakamakon Tashin hankalin da ya biyo bayan harin bom din da aka kai a Zariya da kaduna. An samu labarin Jiya da dadare matasa sunyi ta kai farmaki a junansu da niyyar daukan fansa. Haka kuma yau ma fada ya barke a Unguwanni daban daban a kaduna. Dukda dokar hana zirga zirga da Gwamnan jihar ya saka. A Damaturu ma ta jihar Yobe rikicin ya lafa kuma suma ansa dokar Hana zirga zirga. Mutanen garin dai sun bayyana wannan abin a matsayin Gazawar Gwamnatin tarayya na kasa magance matsalar tsaro.