content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Wednesday, June 20, 2012

MAI MARTABA SARKIN HADEJIA ALH.ADAMU A.MAJE

Image Hosted by ImageTitan.comHADEJIA A YAU! A Ranar Asabat 3/january/1999 Mai martaba Sarkin Hadejia Alh.Abubakar Maje Haruna ya Nada Alh.Adamu Abubakar A matsayin IYAN Hadejia.

kuma shine Iyan Hadejia Na farko a tarihin Hadejia!
kuma Ranar Asabat 20/september/2002 An nada Alh. Adamu Abubakar A matsayin Sakin Hadejia na Goma sha shida (16) karkashin jagorancin Galadiman Hadejia Alh.Habib Adamu.

kuma an nadashi a cikin fadar Hadejia. kwanaki Uku bayan Mutuwar Sarkin Hadejia Alhaji Abubakar Maje. yayi Hawan sallah na farko a Matsayinsa na Sarkin Hadejia wato:

Hawan sallar Azumi Dec. 2002. wato kafin a Bada Sanda. Ranar Asabat 29/March/2003 Akayi bikin bada sanda A filin wasa na Hadejia Karkashin Jagorancin Gwamnan Jigawa Alh.Ibrahim Saminu.

Ranar 14/september/2012 Zai shekara Goma(10) yana sarautar Hadejia.

zamu rinka kawo muku Irin Gudunmawa da ya bayar ta ci Gaban Wannan Masarauta. Daga yanzu har zuwa 14/september Na wannan Shekarar wato 2012. Hadejia A yau.

KADUNA BA LAFIYA


HADEJIA A YAU! Rahotanni daga jihar Kaduna ya nuna cewa Har yau rikici bai lafa ba dukda Dokar hana zirga zirga da aka sanya a Jihar. Ko a yammacin yau anji Karar harbe harbe da kone kone a yankin Badarawa,Unguwar yero da kuma wasu sassa a Unguwar Dosa. Wani ma'aikacin Gidan Redio ya ruwaito cewa An harbi wani yaro a Gabansa, Bayan an kaishi asibiti daga bisani ya cika. Allah ya mana maganin wannan masifa! Kwanaki hudu dai kelau ana zaman Dar dar a Jihar Kaduna Rikicinda ya rikide ya zama na kabilanci da Addini.