content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Monday, July 9, 2012

TARIHIN KAFUWAR HADEJIA KASHI NA (1)






TARIHIN KAFUWAR Hadejia Ya farune daga wani maharbi mai suna Hade, shi wannan maharbi ya taho ne daga yankin Machina ya yiwo yamma har yazo wannan wuri da yanzu ya zama Hadejia. Lokacin da yazo sai ya iske Daji mai bishiyoyi ga kuma Namun Daji da Tsuntsaye ta ko ina, sai ya zauna yaci gaba da farautarsa har saida wata rana yana tafe da karyar sa sai tayi nisan kiwo ko da tazo sai yaga duk jikinta da ruwa, sai yayi mamakin hakan har ma sai yabi sawunta. Koda yaje sai yaga kogi kuma ga tsuntsaye suna shawagi a wurin. Sai ya yanke shawarar zama a wannan wurin, kuma hakan yayi. Anan ya zauna yayi bukkarsa yake harbe harben Namun daji kuma yayi SU,wato kamun kifi. 

In ya kashe namun daji sai yaje ya sayar da fatun. Harma ya dauko matarsa wato Jia ya dawo da ita wannan wurin. Kuma mutane sai suke zuwa sayen fatu da nama a wurinsa. Duk wanda yazo wurin sai yayi sha'awar zama a wurin, haka nan gari ya fara bunkasa wasu maharba, wasu masinta, wasu kuma mafarauta. Sai gari ya kafu kowa yazo wucewa sai ya yada zango a garin. Kuma makwafta masu zuwa sayen Namun Daji sai suke kiran garin da suna Garin Haden-jia, wato suna masa lakabi da sunan matarsa. 

To kasancewar gari sai da shugabanci ne yasa shi Hade ya zama shugaban garin, duk wanda zaije sayen fatu ko nama sai yace na tafi garin Haden jia.
Wato ana masa lakabi da sunan matarsa. To sakamakon takaita kalma irin ta Bahaushe sai aka dunkule sunan ake cewa Hadejia.

Kuma bayan zamanin wannan mutumin
Hadejia taci gaba da zama gari kuma tare da shugabanci wato mulkin Sarakunan Habawa. Kuma a lokacin akwai kananan Garuruwa masu wadda suke kusa da Hadejia kamar Rubban Dakata, Auyo, Hadagwaigwai da dai sauransu. Wadanda suma suna da nasu sarakunan a wannan Lokacin. Kuma Hadejia sunyi Sarakunan Habe guda talatin da biyu(32),amma sunan mutum uku ake dasu wadanda sukayi mulki kafin zuwan Fulani. 
1, BAUDE 
2,MUSA 
3, ABUBAKAR. 

A zamanin Mulkin Sarkin Hadejia na Habe Abubakar fulani sukazo kasar Hadejia, kuma shine ya basu masauki a Hadejia Lokacin Hadejia tana karkashin Daular Borno, domin tana karbar Umarni ne daga Galadiman Borno. Sarkin Hadejia na Habe shi ya nada Umaru a matsayin Sarkin fulanin Hadejia. Wato kafin Jihadin Shehu usman Danfodiyo. Kuma har yanzu fulanin sune suke sarautar Kasar Hadejia.

A GABA ZAN KAWO MUKU TARIHIN
SARAKUNAN FULANI DA DALILIN KARBAR TUTA DA YADDA SUKA TUNKUDE SARAKUNAN HABE DAGA SARAUTA.

THE ORIGIN OF FULANI (Asalin Fulani)


Who Are the Fulani People? Origins The history of the Fulani seems to begin with the Berber people of North Africa around the 8th or 11th century AD. As the Berbers migrated down from North Africa and mixed with the peoples in the Senegal region of West Africa the Fulani people came into existence. Over a thousand year period from AD 900 - 1900, they spread out over most of West Africa and even into some areas of Central Africa. Some groups of Fulani have been found as far as the western borders of Ethiopia. As they migrated eastward they came into contact with different African tribes. As they encountered these other peoples, they conquered the less powerful tribes. Along the way many Fulani completely or partially abandoned their traditional nomadic life in favor of a sedentary existence in towns or on farms among the conquered peoples.

The nomadic Fulani continued eastward in search of the best grazing land for their cattle. Their lives revolved around and were dedicated to their herds. The more cattle a man owned, the more respect he was given.
Today, some estimate as many as 18 million Fulani people stretch across the countries of West Africa. They remain to be the largest group of nomadic people in the world. What Do the Fulani Believe? Religion and Beliefs:

The Fulani were one of the first African tribes to convert to Islam and are today more than 99% Muslim. The devout Muslim Fulani have seen themselves as the propagators and preservers of the Islamic faith in West Africa from as early as the fourteenth century. Historically it was a Fulani chief named Usuman dan Fodio, along with nomadic Fulani herdsmen who were instrumental in facilitating the spread of Islam across West Africa through evangelism and conquest. At times they would wage "holy wars" or jihad in order to extend and purify Islam. As the Fulani migrated eastward they spread their Islamic beliefs. As they became more powerful and attained more wealth they began to be more aggressive with their religion. 

Their adoption of Islam increased their feeling of cultural and religious superiority to surrounding peoples, and that adoption became a major ethnic boundary marker. Some settled in towns and quickly became noted as outstanding Islamic clerics, joining the highest ranking Berbers and Arabs.