"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Sunday, September 23, 2012

HISTORY OF HADEJIA

HADEJIA HISTORY
Prior to the rise of the emirate Council in
Hadejia, the territory now known as Hadejia
Emirate or Kasar Hadejia, was made up of
seven separate and distinct kingdoms namely:
Garun Gabas, Auyo, Dawa, Fagi, Kazura,
Gatarwa and Hadejia. Unfortunately, these
kingdoms possessed neither historical
documents nor codified oral traditions which
could throw light on their histories. Our
knowledge of these Kingdoms therefore
remains obscure and scanty. Available oral
tradition tells us that the rulers of each of
these seven Gudiri States received their titles
from, and owed allegiance to the Mai of
Borno through the Galadima, whose seat was
at Nguru. Furthermore, the same tradition
tells us that Auyo and Garun Gabas were the
oldest of the seven Kingdoms. The kingdom
of Auyo together with Tashena and Shira of
Katagum emirate were said to be founded in
about 1400 A.D. by immigrants from
Baghirmi, while Hadejia and probably the rest
of the kingdoms were founded afterwards.
The founders and early settlers of all the
Kingdoms east of Kano, we are told, were
attracted to this area by its richness in terms
of grazing land, fertile landscape. and fishing
streams. Hadejia town, for instance, owed its
name and origin to a Kanuri hunter from
Machina, Hade, and his wife, Jiya, who, while
on hunting expedition, became attracted to
the area because of its rivers and other
natural endowments. Hade became the
founder of Hadejia and the first in a long line
of Hadejia Kings - thirty-two in all who ruled
the area before the nineteenth century jihad.
Unfortunately, the names of only three of
these kings have been preserved – Baude,
Musa and Abubakar (Gowers, 1921). The
town and the kingdom, and indeed later the
emirate, got their name when Hade and his
wife Jiya settled in the area, and the people in
the surrounding settlements started to
migrate to, or identify the area with, them. It
is said that the people often referred to the
settlement as Garin (town of) Hade and Jiya
and later merged the two names and simply
called it HADEJIYA, after the name of the man
and his wife. Be that as it may, what emerged
from the little we know is that Hadejia
together with the six other kingdoms in the
region were all at one time or the other
brought under the control of Borno Empire.
They constituted what the Bornoans called
the "Nguderi or "Gudiri' territories. They
remained under Borno's imperial control up
till the beginning of the Nineteenth Century
when the Fulani conquered them and
subsequently transformed them into what
became known as the Hadejia emirate.
The founders of the emirate were a group of
nomadic cattle herdsmen who were
descendants of one Hardo Abdure. They were
said to have come from Machina in western
Borno in search of grazing land; and by the
end of the 18th century a sufficient number
of them had settled in the area due to the
availability of rich pasture. Accordingly, owing
to the growing number of Fulani
communities in the area, Sarki Abubakar, the
last Hausa King of Hadejia, appointed one
Umaru B. Abdure as Sarkin Fulanin Hadejia in
about 1788.

Tuesday, July 17, 2012

KASAR HADEJIA DA KABILUN CIKINTA


HADEJIA A YAU! Kasar Hadejia tana da kabilu da dama wadanda kuma suke da yarensu daban-daban: kamar...
1, HAUSAWA
2, ABORAWA (FULANI)
3, MANGAWA
4, GIZMAWA
5, BADAWA
6, KOYAMAWA.

1, HAUSAWA:- Kabilar Hausawa sune kabila mafiya yawa a kasar Hadejia Domin su babu wadda zaice ga wani lokaci da suka shigo Kasar Hadejia, kuma tafi karfi a kasar sakamakon dadewar Garuruwansu. kamar Garun Gabas (Biram), Auyo, da Matsa. kuma ko zuwan Bayajidda Garun Gabas yazo ne ya samu Mutanen Garin suna yin yaren Hausa.

2, ABORAWA (Fulani):- Kabilar fulani sun shigo kasar Hadejia tun a Farkon karni na goma sha biyar (15) kuma sun shigo ne daga yankin Massina wasu kuma daga Katsina, kuma sun Taho ne daga Gabar Kogin SENEGAMBIA wato SENEGAL. Sun fara zama ne a Rinde wasu kuma sun Zauna a Jarmari wasu a Marke wasu a Adiyani da Margadu. Kuma ayarinsu ya kasu biyu Inda wasu suka wuce kasar Kano Karkashin Jagorancin Lamido Usman Kalinwama. A Karni na goma sha Tara (19) Wasu fulanin sun sake shigo Kasar Hadejia daga yankin Machina Karkashin Jagorancin Ardo Abdure Dan Jamdoyi. Kuma ance Kafin suzo Hadejia saida suka zauna a Kankiya ta Jihar Katsina. kuma wadannan fulani suke Sarautar Hadejia har zuwa Yau.

3, MANGAWA:- Kabilar Mangawa ko Barebari wadanda mafi yawancinsu suna zaune a Gabas da Hadejia da kuma Arewacin kasar Sun zo ne A karni na goma sha bakwai (17) sun taho ne daga yankin Borno kuma mafiya yawansu sun zo kasar Hadejia ne Tonon Azurfa da Tagullah. Inda kuma daga baya wasu sun shigo kasar Hadejia A lokacinda RaBe yaci Kukawa da Yaki sai suka kaura suka dawo kasar Hadejia, Kamar garuruwan Birniwa, Baramusa, Kacallari, da Sauransu.

4, GIZMAWA:- Gizmawa suma kamar Mangawa sun shigo ne a Karni na goma sha bakwai (17) kuma suma suna zaune ne a yankin Guri, Marma, Lafiya da sauransu kuma suma yarensu kusan kamar barbarci ne saidai wasu kalmomin da yake canzawa.

5, BADAWA:- Kabilar Badawa basu da yawa a kasar Hadejia, kuma suna zaune ne a Garuruwan Iyakar Hadejia da Bedde, Kamar Gayin, Adiyani, Margadu,da Kadira. wasu sun zauna anan ne tun kafin yakin Gogaram. wasu kuma sunce dama anan suke tuntuni. ganin cewa suna iyaka ne da Kasar Bedde.

6; KOYAMAWA:- Kabilar koyamawa suma basu da yawa kuma Dangin Barebari ne, sai dai zanensu ya bambanta. kuma yarensu ma ba iri daya bane. Kuma suna cewa sun taho ne daga Gabas da Sudan. sannan suna zaune ne a Kasar Kafin Hausa, Bulangu, Yayari, koyamari da sauran garuruwan kasar Kafin hausa.

7; TIJJANAI:- Kabilar Tijjanai fulani ne dake zaune a Yelleman kuma Malamai ne masu bin Darikar Tijjaniyya. shi yasa ake ce musu Tijjanai. Sun shigo kasar Hadejia a shekarar 1903, Daga Malo a yankin Tukolar Senegal. sun taho ne bayan Turawan France sun yiwa Yankinsu Mulkin Mallaka. Sun taho karkashin jagorancin Shugabansu Muhammadu El-Bashir, kuma sun fara zama ne a Lokoja. Magajinsa kuma Ahmadu Madaniyyo sai ya sake tasowa daga Lokoja yazo Kasar Hadejia aka basu Wuri suka zauna. wato Yelleman Tijjanai. Alhamdu lillahi. Hadejia A Yau.