"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Thursday, November 15, 2012

TAKAITACCEN TARIHIN SHETTIMAN HADEJIA DA M. BILYAMINU USMAN.

Easily Upload Your Images To Myspace
Free Musichttp://www.MyspaceImageCodes.net">Easily Upload Your Images To Myspace
Free Music Hadejia A yau! Assalamu alaikum! Barkanmu da shigowa sabuwar shekarar Musulunci. A daidai lokacinda muke kokarin Bankwana da shekarar 2012, Allah cikin Ikonsa wannan shekara tazo mana da wani bubban Rashi wanda bazamu manta dashi ba! Wannan rashin kuwa shine na Alh. Bilyaminu Usman da Alh. Hassan Hadejia (shettiman Hadejia). A ranar Asabat 20/october/2012 Allah yayiwa M. Bilyaminu Usman Rasuwa yana da shekaru 83. Kafin rasuwarsa ya rike mukamai da dama musamman a hukumar Ilmi. M. Bilyaminu ya fara koyarwa a Middle school wato Abdulkadir a shekarar 1948, kuma yayi sakataren Ilmi a Hadejia kuma a shekarar 1976 yayi kwamishinan Ilmi a tsohuwar jihar Kano a lokacin Gwamna Sani Bello. Kuma M. Bilyaminu yayi ministan Ilmi a Jamhuriya ta biyu Lokacin shehu shagari. Kuma ya rike Mukamin Chairman primary Education Board a shekarar 1999. Allah ya kyauta kwanciya. Kuma ya bar mana abin koyi a sha'anin zaman rayuwa, wato Gaskiya da rikon Amana. Ko wadanne Irin darasi muka koya daga Rayuwarsa? Hadejia a yau. http://www.facebook.com/Ismailaasabo Haka kuma Ranar laraba 7/November/2012 Allah yayiwa Shettiman Hadejia Rasuwa Alh. Hassan Abbas, sakamakon 'yar gajeriyar jinya, Shettiman Hadejia tarihin Hadejia bazai manta da irin Gudunmawar da ya bayar ba ta hanyar ci Gaban garin Hadejia da Taimakon Addini, masu iya magana suna cewa ba rabuwa da Gwani ba Maida Gwani. Wannan Haka yake Kasar kago bata Maida Kago. Shettiman Hadejia ya rike mukamin Minista a lokacin Jamhuriya ta daya, bayan nan ya rike mukamin Ministan Man fetur a zamanin Ibrahim Babangida, kuma shine shugaban Kaduna polo club, sannan shine Chairman Board of Directors a kamfanin Leadway Assurance! Sannan Board member A Masallacin sultan Bello dake Kaduna. Allah ya kyauta kwanciya! A cikin abubuwanda ya bari wadanda zamuyi koyi dasu akwai kyautatawa al'umma da taimakawa Addinin musulunci da zumunci. Hadejia a yau. Muna rokon Allah ya bamu Albarkar wadannan mutane, Allah ya maida mana makamantansu, Allah ka kara mana Gaskiya da Rikon Amana da taimakon Al'umma. HADEJIA A YAU.

Monday, November 5, 2012

SULE LAMIDO SAI GODIYA.

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU! Alhamdulillahi Godiya ta tabbata ga Allah wanda yake bada Mulki ga wanda yaso, kuma a lokacinda yaso, Tsira da Aminci su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammadu wanda Allah ya aikoshi da shiriya da rarrabewa tsakanin Karya da Gaskiya!

Bayan haka muna kara Godiya ga Mai Girma Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Dr. Sule Lamido, wanda Allah ya bashi Mulkin Jigawa domin ya Gudanar dashi bisa Gaskiya da Adalci. Alhamdulillahi Jigawa a yau.

Ranar Litinin 5/11/2012. Mai Girma shugaban kasa ya kawo mana ziyara Hadejia a karkashin mulkin Gwamna Sule Lamido, Inda kuma akayi hawan Daba kasaitacciya. Hakika wannan abin Alfahari ne a garemu Hadejiawa kuma babu abinda zamucewa Mai Girma gwamna sai godiya.

Bayanda shugaban kasa yazo Hadejia ya ziyarci fadar Mai martaba Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar Maje, bayan yaga Hawan Daba da aka shirya masa ya gana Da Mai martaba Sarki. Kuma ya nemi Alfarma guda Uku wadda zata kara Inganta wannan yanki na Hadejia. Na farko ya nemi Alfarmar Gwamnati da ta ci gaba da aikin B.E.C. Wanda a halin yanzu ya dakata, na Biyu ya nemi Alfarmar da ayi mana Maganin Ambaliyar Ruwa da ta Addabi wasu sassa na Hadejia.

Na uku ya nemi Alfarmar a Sake Inganta Jingar Kogi wadda ake samun Asarar Dukiyoyi da amfanin Gona.

Muna kara Godiya ga Wannan Gwamnati wadda A zamaninta ne Jigawa ta tabbata Jigawa. Hakika duk wanda yasan Jigawa shekara Bakwai baya Idan yazo zai tabbatarda Jigawa ta samu Uba. Jigawa abar Alfaharinmu, Sule Lamido Abin Alfaharin Jihar Jigawa.

Hakika abubuwanda mukeji a baya kunnenmu ne yaji Idonmu bai gani ba. Dan haka ka bada saida akan abinda Idonka ya gani yafi akan abinda kunnenka yaji. Muna kara jinjina ga Mai Girma Gwamna Wanda ya daga Darajar wannan Jiha tamu. Jigawa ada take Jaririya amma a yanzu Uwace a zamanin Sule Lamido.

Ba rabuwa da Gwani ba Maida Gwani. Jigawa ta tattara Manyan Mutane masu hazaka! kama daga Gwamnan zuwa comishinoni da sauransu. Jigawa tarin Allah Lamido Ikon Allah.

Allah ya huci gajiya, Allah ya maida kowa Gidansa Lafiya. Ameen. Hadejia a yau.