content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Friday, March 15, 2013

KUDUBAR JUMA'A DAGA BUBBAN MASALLACIN HADEJIA.

HADEJIA A YAU. A yau malam Na'ibi yi mana kudubace mai taken :- JIN TSORO DAGA AZABAR ALLAH S.W.T. Fassara:- Ibrahim Umar. Yan uwana musulmai Malam ya ja hankalinmune game da jin tsoro daga azabar Allah Mai Girma da Daukaka domin kamun ubangiji ya kasance mai tsananine. Yan uwana kullun mu cigaba da kasancewa daga cikin bayin Allah Madaukaki masu da'a tare da jin tsoron azabarsa. Kada mu kasance daga bayi azzalumai masu zalintar kansu wajen keta Abubuwan da musulunci ya hana. Manzon Allah S.A.W yana cewa "kuji tsoran wuta ko da da tsagin dabino ne" Ma'ana koda abin da zakayi sadaka dashi kamar tsagin dabinone don ka bayar dashi ka kare kanka daga wuta to kayi kokari ka bayar. ALLAHUMMA INNA NARJU RAHMATIKA WA NAKHAFU AZABAK. ya Allah SWT ka karemu daga azabar wuta amin.

Monday, March 11, 2013

FACEBOOK A KARKARA!

HADEJIA A YAU!Hadejia A yau! Assalamualaikum! 'Yan uwa barkanmu da yau, da fatan Alkairi. muna gaf da fara wani shiri a wannan shafi na facebook. shirin kuwa zai leka ne loko na kauyukan Arewacin Nigeria, domin jin halin da talakawa suke ciki a kauyuka da karkara. domin wasu kauyukanma ba'a kulasu sai an buga gan-gar siyasa. Sanin kowane Talakawa akar-kara suna cikin mawuyacin hali fiye da na biranen Arewacin Nigeriya. Ada sashin hausa na gidan redion b.b.c. yana gudanar da wannan shiri wanda kuma yin hakan na sanya gwamnati ta gyara kura-kuranta. To amma yanzu shiru muke ji ba labari. Hakan yasanya mu yin azama wajen gabatar da wannan shiri ta hanyar fcbk. kasancewar shugabanni na amfani da shafin na fcbk. Duk da ma dai sunsan halinda ake ciki to amma fadawa duniya zai kara sanyasu su gyara. Kaima kema zaku iya shiga wannan shiri ayi da ku domin yin hakan jihadi ne bubba wanda Allah ne kadai yasan ladan da zaka samu. Domin ka yi sanadiyyar fitar miliyoyin alumma daga cikin Kangin talauci. Duk mai bukatar ayi wannan aiki da shi ya Tuntubi Garba Tela Hadejia ta inbox. Ko ya kira lambarsa ko ya masa sakon Wasika (text). 07065540705. Allah ya bada Iko.