content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Saturday, March 23, 2013

HADEJIA EMIRATE

HADEIJA A YAU.

Authority : Mr. A. Campbell-Irons.

The Emirate of Hadejia contains an area of 2,768 square miles, and is divided into six Districts. It is situated to the north-east of Katagum, in the Northern Division. It is a disputed point whether in the tenth century.

Hadeija or Gobir formed one of the seven Haussa States. In the Kano Chronicle there is a mention that the son of the Sarkin Machina came to Kano in the reign of Yakubu (1452-63) and was made Chief over Hadeija, with the title of Sarkin Gabbas.

It became a Fulani Emirate at the time of the Jihad, Sambo receiving a flag from Othman Dan Fodio. His elder son Buhari made himself King in defiance of the Sarkin Musulmi's edict in favour of his younger brother ; and, obtaining the support of the Shehun Bornu, defeated all opponents. His reign was one long succession of wars and he was finally killed in battle at Gorgaram about 1863.

Hadeija sent in submission to the British in 1903. In 1904 the British occupied the country, but the fifth Chief opposed their advent and was overthrown and killed in 1906, and Haruna appointed in his place. He died in 1909, and was succeeded by the Chiroma Abdulkadir.

In that same year the Beiyut-el-Mal (Baitilmalu) was started.

The population number some 115,448, and consists of Kanuri, Fulani, Auyokawa, Maguzawa from Kano, Koyamawa, Beddawa, Ngizimawa, Mangawa.

There is a town of historic interest in Hadeija named Garungabas, but which in old times bore the name of Biram, which was originally of great influence. It was founded by Arabs from Bagdaza or Baghdad. One Muktari, or Bayajibda, with his younger brother Biram, Migrated west until they reached Birnin Bornu (Kukawa), where the Shehu gave Muktari a town and his daughter in marriage. Muktari was presently compelled to flee, but left his wife on the road, where she gave birth to Biram, who founded Garin Gabbas, Muktari continuing his journey as far as Daura, where he slew the celebrated serpent and married the Queen.

Another version of the legend is that it was Buram, the younger brother, who founded Garingabas.

A descendant of this Arab family still reigns as Chief. Hadejia A yau.

Tuesday, March 19, 2013

TAURARINMU (HADEJIAWA) Part two (2)

Image Hosted by ImageTitan.com Hadejia A yau! Daga M.MUHAMMAD IDRIS.. A cigaba da kawo muku Takaicaccen tarihin wadanda suka bada Gudunmawa a kasar Hadejia, yau mun tabo Mutum Uku wadanda tarihin Hadejia bazai manta dasu ba!


AIR VICE MARSHAL HAMZA ABDULLAHI(RTD) *************** AVM Hamza Abdullahi. Daya daga manyan hafsoshin soja na kasa, daya daga cikin manyan arewa, tsohon Gwamnan Jihar kano, tsohon ministan Abuja, tsohon ministan aiyuka na musamman. Avm Hamza yayi mulki na wata 18 amma ya yi aiki na mamaki a fadin jihar kano.


Aiyukan da suka shafi masarautar Hadejia sun hada da: ginin hanyar Bulangu da Guri, ginin Asibitin Birniwa, K/Hausa da Bulangu, ginin makarantun mata na kaugama da Birniwa, ginin kwaltocin cikin garin Hadejia da gina fadar Hadejia ta zo daidai da zamani. karin streets light. .


Lokacin yana ministan Abuja ko 'yan kwangila da dama sun samu aiki, manyan mutane da yawa sun samu fulotai, ya samarwa matasa karatu a institute of management ta Abujan.


Avm Hamza bayan ya bar Gwamnati ya ci gaba da bayar da gudunmawa domin ci gaban al'ummarsa ya gina katafaren gida domin saukar bakin kunya, ya gina masallaci na juma'a mahadi ka ture ya kuma tanaji makeken fili a yamma da masallacin domin gina makaranta, yana kawo masu Likitocin ido domin masu larurin ido.


Avm yana daukan yara masu karamin karfi ya kaisu Turkish School in sun gama ya nema musu admission a kasa ko a waje,yanzu haka akwai yara biyu a kasar Turkey wanda shi yake daukan nauyinsu. Tsakanin Avm. da masarautarsa akwai kauna domin ba sallar da za ta zo bai yi ta a Hadejia ba sai in ba ya kasa. Muna masa fatan alheri da karuwar arziki mai amfani.



ALHAJI BELLO IBRAHIM AUYO **************** Marigayi Alhaji Bello Ibrahim Auyo. "Agogo sarkin aiki" tsohon malamin makaranta, gogaggen dan siyasa. Ya fara aiki tun daga malamin makaranta har ya kai mukamin sakataren ilmi.


Ya rike mukamin kwamishinan zabe tun muna jihar kano. Ya yi shugabancin karamar hukumar Hadejia har sau biyu. Shi ne shugaban ALGON na kasa.


Alhaji Bello Ibrahim ya fi kowane shugaban karamar hukuma da aka yi a Hadejia aiyuka na raya gari. Alhaji Bello Ibrahim ne ya gina sakatariyar karamar hukumar Hadejia da ake cikinta, shi ne ya gina Asibitin Kofar Arewa da shagunan bayanta, shi ne ya gina kasuwar jan bulo. Bello ya dauki ma'aikata da malaman makaranta masu yawa a zamaninsa. A zamaninsa matasa masu yawa sun samu muhalli domin ya raba filaye da dama a wurare masu yawa.

Misali shi ya raba filin idi kuma ya sanyawa wurin suna Unguwar Mu'azu Hadejia,


ya bayar a fanisau kuma shi ya sayarwa mutane gidajen fanisau, ya raba a gabari, ya raba a Gandun Sarki.

Bello ya yi ginan magudanan ruwa ba adadi a Hadejia. Yayi aiyuka a Auyo lokacin muna hade da ita.

"Turmin tsakar gida sha gwagwarmaya"
Bello mutum ne mai riko da addini, jam'i ba ya wuce shi, ya rike dangi musamman marayu, da azumi a bakinsa Allah ya karbi ransa. Allah ya sa ya sha ruwa a Aljanna, ya yafe masa kura-kuransa.......



ALHAJI ADAMU KWANO *************** Alhaji Adamu kwano tsohon ma'aikacin lafiya ne wanda ya bayar da gudun mawa matuka a wannan fage. Allah ya yi masa fikira kwarai domin shi ba likita ba ne amma yakan yi aikin da ya gagari likitoci.


Adamu kwano ya shahara akan kaciya domin galibin matasan Hadejia da kewaye daga 'yan shekara 30 zuwa 50 duk yawanci shi ya musu shayi.

Alhaji Adamu kwano attajiri ne mai son ci gaban addini, shi ne ya gina makarantun islamiya ta Hudu da Garko da makarantar sakandire ta Aminu Yusuf.

Adamu kwano shi ne mutum na farko da ya yi kokarin gina Asibiti mai zaman kanta sai dai ba ta fara aiki ba Allah (SWT) ya yi masa rasuwa.

Muna rokon Allah(SWT) ya ji kansa yaarzurta mu da masu hali irin nasa. AMEEN.