"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Friday, April 5, 2013

KHUDUBA DAGA MASALLACIN FANTAI HADEJIA...

Image Hosted by ImageTitan.comHADEJIA A YAU! Daga Yaya Ilallah.


~~~ZUWA WAJEN BOKA~~~


Alhamdulillahi Rabbil Alamin. Muna farawa da sunan Allah wanda da Ikonsa komai ya kasance, da kuma Abinda zai kasance! Tsira da Aminci su tabbata ga Manzonsa Muhammadu s.a.w. Wanda ya aikoshi da zance mafi dadi wato Alqur-ani.


Alhamdulillahi Yau khuduba daga Masallacin Usman Bn Fodio dake cikin makarantar Fantai daga bakin Mal. Bashir Muhd Baima, ta yi magana ne ga hani zuwa wajen:- BOKA ko YAN TSUBBU. Wadda a lokacin yanzu shedan ya kada gangarsa wajen haska zukatan ashararu daga cikin mutane kamar 'yan siyasa, masu mulkin gargajiya da na gwabnati da kuma masu rike da wasu mukamai.


Manzon Allah s.a.w yace: Duk wadda ya je wajen Boka, ba za a amsa masa Sallarsa ta kwana 40 ba. In kuma ya yi imani da abun da ya fada, to ya kafurta da abun da Annabin ya zo da shi. Wani abu mafi muni da takaici, za ka ga matasa maza da mata na neman taimakon Bokaye wai da sunan Farin jini, neman mulki, mallakar miji da kokarin mallakewa zuciyar abokin soyayya ga samari da 'yan mata.


Haka dabi'ar ta kara watsuwa cikin zukatan wasu jahilai ta yadda in wani abu na musiba ya samesu , sai su tafi ga Boka don gano yadda wannan abu ya faru a gareshi. Ya manta da Allah ne ya Qaddara masa. Toh Allah kyauta.


Masu irin wanga dabi'a Allah shiryesu, mu kuma Allah ya karemu. Amen.

Monday, March 25, 2013

TAURARINMU (HADEJIAWA) PART THREE (3)

HADEJIA A YAU.


DAGA M. MUHAMMAD IDRIS HADEJIA.


SHEIKH USMAN KADUNA *************** ­ Sheikh Usman Kaduna,daya daga cikin manyan malaman Jihar Jigawa,kololuwa­r malunta a masarautar Hadejia, daya daga cikin jigogin "council of ulama" na jihar jigawa, shehi kuma madugun tafiyar Darikar Tijjaniya a masarautar nan. Gaba daya rayuwar malam akan yada ilmin addini ta kare.

Malam ya yi aiki a L.E.A a matsayin babban inspector na Arabiya.Ya sha yin Board Member a Hukumar Alhazai ta jiha.

Gidan malam jami'a ce ta masarautar Hadejia. Malam malamin malamai ne domin duk wani malami mai shekaru saba'in zuwa kasa in malam bai karantar da shi ba to ya karantar da malaminsa. Malam ­ ya yi nisa a fagen bayarda ilmi domin har daga kasashen ketare ana zuwa wannan jami'a tasa.


Almajiran malam ne suka fara kafa Islamiya ta dare domin magance hira marar amfani da matasa kan yi a cikin wannan gari.

Malamyana gabatar da tafsiri a kowane watan azumi a dukshekara wanda ke samun halartar jama'a masu yawa. Bayan karantarwa ta yau da kullum malam yana karantar da hadisi a ranar kowace juma'a tsakanin magariba da isha'i. Allah ya karawa malamlafiya ya kuma ba shi ladan Ayyukanda yake na Alkairi.


ALHAJI HASHIMU AMAR(WAZIRIN HADEJI)*************** ­* Alhaji Hashimu Amar yana daya daga cikin tsofin 'yan bokon wannan masarauta, ajins­u daya da marigayi sarkin Hadejia Alh. Abubakar maje tun daga firamare har midil (Middle).


Alhaji Hashimu Amar a"internal revenue" ya yi aikinsa har ya kai kolokuwawato babban Darakta kuma anan ya yi ritaya. AlhajiHashimu ya dauki ma'aikata matuka a wannan masarauta har ma da wajenta.

Alhaji Hashimu dattijo ne mai gaskiya da rikon amana ya kare mutuncinsa da na masarautarsa matuka don haka wajen daukan aikinsa bai nuna kabilanci ba, babu ruwansa da kusa ko nesa, ko na gari ko kauye.

Wannan ya kara masa mutunci matuka a wannan masarauta. Alhaj­i Hashimu ya zama wazirin Hadejia a lokacin Marigayi Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje kuma kullum yana hanya domin samo ci gaban wannan masarauta.

Hadejiawa suna masa addu'a Allah ya albarkanci zuriyarsa.