content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Thursday, August 8, 2013

HAWAN SALLAR AZUMI NA 8/8/2013 ALHAMIS.

Hadejia A yau. Daga Muhd Yawale Hadejia >


kamar yadda Aka sani Hawan sallar Azumi yana da tarihi mai tsawo a cikin Garin Hadejia, wannan sallar ma A bisa al'adar masarautar hadejia ranar sallah maimartaba sarki zai fito daga gida da safe, akafa tareda sauran mutanan fada domin zuwa filin idi. Dukda cewa za'ayi sallar ne a Bubban Masallacin Juma'a na cikin gari. Sakamakon ruwan sama da akayi kuma yayi ta'adi, Mai martaba sarki ya dage Hawan sallah domin Jajantawa ga wadanda ruwa yayi musu ta'adi.


Ga bayanin yanda Hawan sallah yake kasancewa da kuma ta Gurarenda ake bi. Bayan an idar sallar idi liman ya kammala huduba,sai hakimai da sauran mahaya dawaki su hau, sannan maimartaba shima zai hau dokinsa tare da Dandalmu, zai bi ta kasuwar kuda zuwa Titin yahai zuwa makera, sannan zai bi ta makwallah zuwa kofar Liman.


Idan maimartaba sarki yazo daidai kofar liman yakan tsaya domin karfar Jafi daga Hakimai. Wanda hakan ta samo Asali ne Tun Lokacinda Sarkin Hadejia Muhammadu Mai shahada ya dawo daga Yakin Madarumfa, ya tsaya a wannan Gurbin Inda su Jarumansa suke zuwa suke masa Jinjina. Amma a lokacin yana Hakimi ne kafin ya zama sarki. Bayan ya zama sarkin Hadejia sai ya maidata Al'ada wato duk sallar Azumi da Layya zai tsaya Hakimai suzo suyi masa jafi.


Daga nan kuma sai maimartaba sarki ya karasa rumfar manyan baki domin gabatarda jawabin sallah, bayan nan kuma sai maimarta ya karasa gida ya sauka tareda sauran hakimai.


Wannan shine Bayanin Hawan sallar Azumin wannan shekara a takaice da fatan Allah yasa ayi hawa lafiya a sauko lafiya. Allah yaja zamanin maimartaba sarki.

Saturday, August 3, 2013

TAKAICACCEN TARIHIN SHEIKH ISAH WAZIRI (WAZIRIN KANO)

HADEJIA A YAU!
Shekh Isah Muhammad Gidado wanda akafi sani da Mallam Isah Waziri.. An haifeshi a cikin garin Kano a shekarar 1925, kuma Da ne ga Wazirin kano Muhammadu Gidado. Yayi karatunsa na Allo a ciki da wajen kasar kano, sannan ya halarci makarantar koyon Aikin Shari'ah a cikin garin kano, daga bisani ya tafi Jami'ar Al-Azhar dake Egypt Inda ya karasa karatunsa. Kuma ya samu ilmin shari'ah da Koyarda Ilmin Addinin Musulunci.




Bayan ya gama karatunsa Sheikh Isah Waziri ya dawo kano inda ya fara aiki a Ma'aikatar Shari'ah ta kano, a matsayin Clerk daga bisani ya zama Registrar. kuma ya fara Tafsirin Alqu'ani mai tsarki a Garin Zakirai ta karamar hukumar Gezawa a wancan lokacin.




Bayan ya bar Aikin Gwamnati Mai martaba Sarkin kano Alh. Ado Bayero ya nadashi Limamin Masallacin Murtala dake kano, kuma anan yaci gaba da Tafsirin Alqur'ani mai girma. Shekh isah Waziri ya bada gudunmawa da dama a cik da wajen kano wajen Daukaka Addinin Musulunci, kuma yayi kokari wajen ganin anyi aiki da Shari'ar Musulunci a kasar kano ganin cewa Mafiya yawansu musulmi ne!




Sheikh Isah Waziri ya samu wannan sunan ne a lokacin yana Makarantar koyon aikin Shari'a Inda wani Malaminsu mai suna Sheikhul-Bashir yake fada masa ganin cewa Da ne ga Wazirin Kano Gidado. A maimakon yace masa Isah Muhammad Gidado, sai ya takaita sunan yake kiransa Isah Waziri.




Bayan da Limamin kano Kuliya ya tafi Aikin Ambasada a shekarar 1998, Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Ado Bayero ya nada Shekh Isah Waziri a Matsayin Bubban Limamin Kano. Sannan daga bisani An nadashi Wazirin Kano bayan da Dan-uwansa Wazirin Kano ya rasu.




A yau Juma'a 2/8/2013 azumi yana 24 Allah yayiwa Sheikh Isah Waziri rasuwa. Muna rokon Allah ya Gafarta masa ya kyauta Makwancinsa. Muma in tamu tazo Allah yasa mu cika da Imani.