content="3wuzvociws0zc1ytgiyfl4yav6jy8f" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Friday, August 15, 2014

TARIHIN DAN-AMAR DIN HADEJIA M. USMAN GINSAU.

MARIGAYI DAN AMAR ( ALH. MALAM GINSAU) 1917 -1997……………………………..
Marigayi Dan Amar din Hadejia Alhaji Malam Usman Ginsau dan Chiroman Hadejia Ali, dan Sarkin Hadejia Haruna Maikaramba dan Sarki Muhammadu Maishahada ne. Yayi karatun makaranta a garin Hadejia.Yana daga cikin yan makaranta na farko da suko ka bude Clerical College da ke Congo a garin Zaria, kafin ta rikide ta koma ABU Zaria.

Malam ya koma England (UK) domin karin karatu a harkar Community Development. Marigayi Dan Amar ya zama Community Dev. Secretatry na Hadejia N.A. Bayan wannan aiki Marigayi ya kama aikin Gona gadan gadan har zuwa1980.

Ya zama Representative Na Hadejia NA a Old Kano State wanda ya bashi damar shiga Co -operative Society na Nigeria shi da Sarkin Ringim Alh. Sayayadi Mahmudu.Marigayi ya zama 2nd Vice President na Co-operative Society of Nigeria. Yayi Ritaya daga wannan aiki a 1980.

Daga nan Marigayi ya kafa Makarantar Islamiyya da ta Karatun Alkura’ani a Gidansa, shi da kansa yake karantar da mutane, wato manya da yara. Malam yayi ta yin wannan aiki har zuwa 1983 a lokacin da aka nada shi Dan Amar din Hadejia, Hakimin Kafin Hausa.Malam yana daya daga cikin dattijan da suka tsaya wa Kasar Hadejia da addu’a da kuma bada gudummawa wajen duk wani aiki na dattako a Kasar Hadejia. Malam ya rasu ya bar ‘ya ‘ya ashirin da shida.. Daga cikinsu Akwai Dan-Amar din Hadejia na yanzu Alh. Aliyu Usman Ginsau, Hakimin Kafin-hausa, da Baraden Hadejia, Alh. Haruna Usman Ginsau.

Allah ya jikansa ya gafarta masa, ya kara sa albarka a zuriyar da ya bari. Ameen.Posted from WordPress for Android via Hadejia A yau.

Monday, March 17, 2014

TARIHIN JARMAN HADEJIA ALH. ABBA SAMBO (DAGA NA GABA PART FIVE 5)

TAKAITACCE TARIHIN MAIGIRMA JARMAN HADEJIA ALH. ABBA SAMBO!!
Daga Muhammad Yawale.




An haifi Alh. Abba sambo a shekara ta 1943 a cikin garin hadejia, ya fara karatun allo a matakin karatunsa na farko sannan lokacin ya isa shiga makarantar boko. Ya fara da hadejia junior elementary school dake dalla wanda a yanzu ake kira Abdulkadir primary school a shekarar 1953-1957 a garin hadejia. Bayan ya kammala wannan makarantane ya samu shiga middle school a cikin shekarar 1957-1959, daga nan bayan kammala middle school ya koma makarantar horan malamai ta wudil/bichi teachers collage a shekarar 1960-1965.


Bayan kammala wannan karatune ya samu zama headmaster a garin gabas primary school a shekara ta 1966-1971, ya koma karin karatu a advance teachers collage zaria a cikin shekara ta 1971-1974 wanda ya samu certificate in education (NCE). Bayan kamamala (NCE) bai tsaya ba domin samun degree na farko a fannin physical Health Education (PHE) wanda ya kammala a 1975-1978 ABU Zaria. Yayi hidimar kasa (NYSC) a federal advance teachers collage dutsinma katsina state daga 1978-1979.

Wasu ayyuka da yayi:
(1) mataimakin shugaban wasannin motsa jiki gwamnatin tarayya (NSSF) 1985-1989
(2) wakili a hukumar ilimi mai zurfi ta jami'ar Ahmadu
bello dake zaria 1988-1991 
(3) wakilin tantance jarabawar dalibai na kasashen africa 1995. 

(4) shugaban wasannin motsa jiki na makarantun jihar jigawa.


Mukaman da ya rike: (1) shugaban makarantar primary ta garun gabas.(2) jami'i mai kula da shiyar kudu maso yamma wadda take birnin kudu a jihar kano (3) mataimakin shugaban kwalejin makarantar horarda malamai dake garin hadejia (4) mataimakin jami'in ilimi na shiyoyin kananan hukumomin gezawa, da minjibir a jihar kano (5) shugaban makarantar sakandiren jeka ka dawo dake kazaure (6) shugaban kwalejin horar da malamai ta garki. Da sauransu.

Jarman hadejia ya bar aiki ranar 30th ga watan oktoba, 2001 a matakin aiki na 16/17. Bayan rasuwar marigayi jarman Hadejia Alh. Usman sambo na (2) a ranar Asabat 4 ga watan december 2010, maimartaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar maje Con, ya nada ALH. ABBA SAMBO a matsayin JARMAN HADEJIA na (3) a gidan Tafarki Guruza, Jarman Hadejia na biyar (5) a jerin Sarautar Jarma a kasar Hadejia kuma Dan majalisar maimartaba sarki.
HADEJIA A YAU....