"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Wednesday, August 5, 2015

JAWABIN MAI MARTABA SARKIN HADEJIA ALH. ADAMU ABUBAKAR YAYINDA AKA TABBATAR DASHI CHANCELLOR A UNIVERSITY UYO.

Hadejia A yau!


JAWABIN MAI MARTABA SARKIN HADEJIA ALHAJI ADAMU ABUBAKAR MAJE C.O.N. A LOKACIN DA AKA TABBATAR MASA DA MATSAYIN CHANCELLOR NA UNIVERSITY OF UYO. A RANAR LARABA 3/AUG./2015.

Ya fara da yabo da godiya ga Allah (swa.), sannan ya gabatar da vice chancellor na University of Uyo da tawagarsa da sauran manyan baki. Yace nayi farin ciki da jin dadi game da zuwanku Hadejia domin tabbatar dani a matsayin Chancellor na wannan makaranta wadda kuke shugabanta. Yace Bazan manta ba wata rana nayi tafiya zuwa Amurka sai naji wani ya kirani a waya yana sanar dani cewa yagani a Jarida an bani Chancellor a University ta Uyo, nayi mamaki matuka da gaske saboda banyi tunanin haka a zuciyata ba. Sannan nayi godiya ga Allah (swa.) wanda da ikonsa da kudirarsa ne hakan ta kasance.

Ina farin cikin tabbatarwa Gwamnati da kuma Al’ummar Nigeria cewa zamuyi aiki da gaskiya ba tare da banbanci ba domin mun kasance kasa daya Al’umma daya. Wani abin Alfahari shine ita wannan Jami’a ta kasance a yankin da na fara karatuna na Secondary, saboda ina daya daga cikin wadanda sukayi federal government college, Ikot-Ekpene. Kuma na dawo gida zan tallafa ga abinda aka tallafa min.

Babu bukatar inja dogon zance saboda Bakinmu yau zasu koma kano domin su hau Jirgin da zai kaisu Abuja, lalle ina mai farin cikin da kuma godiya gareku domin zuwa da kukayi kasar Hadejia don ku gabatar min da wannan abin Alkairi wadda bazan taba mantawa ba a rayuwata. Kuma zanyi amfani da wannan dama in gabatar da godiyata ga wadanda suka samu damar Halartar wannan taro domin tayani murna. Kuma ina rokon Allah (swa.) ya maidaku gida lafiya tare da duk wadanda suka halarci wannan taro.
NAGODE……..

Mai Martaba Sarkin Hadejia shugaban Majalissar Sarakunan Jihar Jigawa…
Alhaji Adamu Abubakar Maje C.o.n.

Thursday, May 14, 2015

YAN GUDUN HIJIRA...



YAN GUDUN HIJIRA!
Tun a lokacin da rikicin Boko Haram ya Addabi jihohin Borno da Yobe aka samu watsuwar 'yan gudun hijira a wasu sassa na Nigeria, ciki harda jihar Jigawa, kuma akasarin wadannan 'yan gudun hijira zakaga Mata ne da kankanan yara wadanda mafiya yawa suna a kasar Hadejia da kasar Gumel. A lokacin da suka fara zuwa wadannan yankuna saboda basu da abinda zasuyi dole wasu daga cikinsu suke bin masallatai da majlissai domin neman abinda zasuci abinci da yaransu. Abin tausayi zakaga yara da basu fi shekara 7 zuwa 10 ba suna bi kantuna da wurin zaman jama'a suna neman taimako, a kwanakin baya basuyi yawan da ya wuce kaga biyu ko uku ba a kullum amma yanzu abin sai karuwa yake wanda a kalla sai kaga goma zuwa sama a rana daya da mata da kananan yara abin tausayi. zaka gansu a kofar masallatai da kasuwa har da Bankuna wurin layin Atm. Dole mumini mai Imani ya tausayawa rayuwar wadannan bayin Allah domin ba a son ransu suka bar gidajensu da 'yan uwansu suka zo suke yin Bara ba! Saboda yawan kwararowarsu yasa jama'a sun fara kosawa ganin abin ya zama ba na kare ba, yanzu kullum a baka gansu a gidanka ba kaga biyar ko shida.

MASU HANNU DA SHUNI....

Hakika Masu hali sai sunyi amfani da damar da Allah ya basu wajen taimakon wadannnan bayin Allah da muhalli da Sutura da Abinci, da kuma kula da rayuwarsu musamman kananan yaran. yana da kyau masu hali su ware wani abu daga cikin Dukiyarsu don taimakon wadannan bayin Allah a matsayin Sadakatul-jariya.

GWAMNATI MAI JIRAN GADO...

Koda yake bani da masaniya game da yunkurin da Gwamnatin Jigawa tayi game da wadannan bayin Allah, kuma ban taba ganin wani wuri da aka ware don 'yan gudun hijira ba zanso in bada shawara ga Gwamnati mai jiran Gado, A karkashin mulkin ko jagorancin Jam'iyyar Apc, dasu fara duba wannan Matsalar ta 'yan Gudun Hijira kafin su fara Aiwatar da kowane Aiki domin ceto rayuwar wadannan Mata da kananan yara daga yin Bara, wanda hakan ya fara jefa wasu daga cikinsu zuwa ga halaka. An fara samun rade radin wadannan mata 'yan gudun hijira sun fara yin Arangama da wasu gurbatattun mutane suna yin lalata dasu suna basu kudi, har ma ance wasu da yawa sunyi cikin shege Allah ya kiyaye! Abin takaici sai kaga idan 'yan Hisbah suka kama mace tana lalata in suka bincika sai kaga 'yar gudun hijira ce. Kasan Dalilin da yasata cikin wannan hali?

SHAWARA GA GWAMNATI....

Ina bada shawara ga Gwamnati mai jiran gado da suyi la'akari da wannan matsalar domin su san ta yadda zasu bullowa wannan Al'amari, ya kamata Gwamnati ta samar musu mahalli na wucin gadi sannan ta sanya yaransu a Makaranta don ceto rayuwarsu. kuma Ina baiwa Gwamnati Shawara da ta sama musu sana'oi domin su dogara da kansu. misali Gwamnati zata iya amfani da makarantar koyon sana'a don koyawa Matan yanda ake yin SABULU, SAKA, DINKI,Da sauransu. Daga karshe ina Rokon Allah da kar ya nuna mana makamanciyar wannan Bala'i da zai sa mutum ya bar gidansa da iyalinsa ya tafi wani wuri yana yin abinda ko a Addini yana daga cikin Abu mai Kaskanci. Allah ka zaunar da kasarmu da Jiharmu lafiya.

Ismaila A Sabo Hadejia.
13/may/2015.

posted from Bloggeroid