"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Tuesday, October 6, 2015

TAKAITACCEN TARIHIN RAYUWAR CHIROMAN HADEJIA. ALH. AMINU HARUNA

Daga Muhammad Yawale....
.

text-align: center;">

Bismillahirrahmanir-rahim.
An haifi Alh Muhammadu Aminu Haruna a garin Guri a shekara ta 1943, A lokacin mahaifinsa Alhaji Haruna Abdulkadir yana Chiroman Hadejia Hakimin Gundumar Guri. Ya halarci makarantar kur'ani wato allo a garin Guri makarantar sule Gangaran a 1952-1956, ya halarci makarantar Elementary primary Dallah a cikin garin Hadejia a 1953-1956, ya halarci makarantar middle school ta fantai hadejia a 1957-1960, sannan ya halarci makarantar horarda malamai ta Bichi a shekara ta 1960-1962.
Marigayi ciroman Hadejia yayi karatu a potiskum (s.t.c sage 1) a 1970 yayi karatu a kaduna polytechnic (stage2-3) a 1971-1974 yayi karatun higher diploma a zaria Insitute of Administration (A.B.U) a 1979-1980. Ya halarci tarurruka na karawa juna sani a wurare daban daban na kasarnan.

AYYUKAN DA YAYI:
Yayi malamin makaranta a lokacin (N.A) ta Hadejia na tsawon shekaru 2, a karkashin tsohon Head master marigayi Alh Abdu maigari Tafidan Hadejia, yayi malamin makaranta a primary ta dubantu a 1965, yayi sakataren karamin minista na MADAKIN Hadejia Muhammadu Gauyama, a ma'aikatar tsaro ta kasa a lagos bangaren jiragen sama (Air-force) a shekarar 1965-1966,
Yayi malami a kotun babban alkali lokacin alkali Dahiru. A shekarar 1966-1968, yayi malamin Turakin Hadejia lokacin Turaki Adamu, yayi Akawu a ma'aikatar mulki ta (N.A), yayi sakataren karamar hukuma a wadannan wurare Bichi, ringim, gumel, wudil, babura, gezawa, kafin hausa, dawakin tofa yayi sakatare na musamman a karamar hukumar birni da kewaye (kano municipal council).

Ya rike mukamin DPM a kananan hukumomin garki, malam madori, Taura a inda yayi ritaya. Marigayi Sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje Haruna ya nadashi Tafidan Hadejia Dan majalisar sarki a shekara ta 1994, cikin yardar Allah kuma Sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar ya nadashi Chiroman hadejia a ranar asabar 13 ga watam march 2004 a inda ya gaji yayansa chiroman Hadejia Alh. muhammad Abbas.

Marigayi chiroman Hadejia mutum ne mai jajircewa kan gaskiya da rikon amana akan harkar da aka dorashi kuma ya nemawa mutane da dama aiki a lokacin gwamnati kuma duk abinda ya gani ba daidai ba baya yin shiru sai yayi magana hakazalika bai yarda kayimasa zancen waniba. Marigayi chiroman Hadejia ya rasu ranar juma'a da daddare 03/10/2015 bayan ya sha fama da jinya muna rokon Allah ya jikansa ya kuma kyautata bayansa.

Wednesday, August 5, 2015

JAWABIN MAI MARTABA SARKIN HADEJIA ALH. ADAMU ABUBAKAR YAYINDA AKA TABBATAR DASHI CHANCELLOR A UNIVERSITY UYO.

Hadejia A yau!


JAWABIN MAI MARTABA SARKIN HADEJIA ALHAJI ADAMU ABUBAKAR MAJE C.O.N. A LOKACIN DA AKA TABBATAR MASA DA MATSAYIN CHANCELLOR NA UNIVERSITY OF UYO. A RANAR LARABA 3/AUG./2015.

Ya fara da yabo da godiya ga Allah (swa.), sannan ya gabatar da vice chancellor na University of Uyo da tawagarsa da sauran manyan baki. Yace nayi farin ciki da jin dadi game da zuwanku Hadejia domin tabbatar dani a matsayin Chancellor na wannan makaranta wadda kuke shugabanta. Yace Bazan manta ba wata rana nayi tafiya zuwa Amurka sai naji wani ya kirani a waya yana sanar dani cewa yagani a Jarida an bani Chancellor a University ta Uyo, nayi mamaki matuka da gaske saboda banyi tunanin haka a zuciyata ba. Sannan nayi godiya ga Allah (swa.) wanda da ikonsa da kudirarsa ne hakan ta kasance.

Ina farin cikin tabbatarwa Gwamnati da kuma Al’ummar Nigeria cewa zamuyi aiki da gaskiya ba tare da banbanci ba domin mun kasance kasa daya Al’umma daya. Wani abin Alfahari shine ita wannan Jami’a ta kasance a yankin da na fara karatuna na Secondary, saboda ina daya daga cikin wadanda sukayi federal government college, Ikot-Ekpene. Kuma na dawo gida zan tallafa ga abinda aka tallafa min.

Babu bukatar inja dogon zance saboda Bakinmu yau zasu koma kano domin su hau Jirgin da zai kaisu Abuja, lalle ina mai farin cikin da kuma godiya gareku domin zuwa da kukayi kasar Hadejia don ku gabatar min da wannan abin Alkairi wadda bazan taba mantawa ba a rayuwata. Kuma zanyi amfani da wannan dama in gabatar da godiyata ga wadanda suka samu damar Halartar wannan taro domin tayani murna. Kuma ina rokon Allah (swa.) ya maidaku gida lafiya tare da duk wadanda suka halarci wannan taro.
NAGODE……..

Mai Martaba Sarkin Hadejia shugaban Majalissar Sarakunan Jihar Jigawa…
Alhaji Adamu Abubakar Maje C.o.n.