"" /> HADEJIA A YAU!

Ismaila A sabo Hadejia

Ismaila A sabo Hadejia
(1)Wannan dai shine Hotona, wadda Idonku yake kallona. (2) Bayan na tafi gun Sarkina, zaku tuna ni watan wata rana. (3) In wani yayi kiran sunana, sai ku cane Allah yaji kaina. (4) Koda zakuyi jimamina, sai ku yimin addu'ah bayana. Marigayi Aliyu Akilu.

Friday, July 15, 2016

SIR AHMADU BELLO'S CHRISTMAS MESSEGE IN 1959...


“We are people of many different races, tribes and religions, who are knit together by common history, common interests and common ideals. Our diversity may be great but the things that unite us are stronger than the things that divide us. On an occasion like this, I always remind people about our firmly rooted policy on religious tolerance. Families of all creeds and colour can rely on these assurances. We have no intention of favouring one religion at the expense of another. Subject to overriding need to preserve law and order, it is our determination that everyone should have absolute liberty to practise his beliefs.

It is befitting on this momentous day, on behalf of my ministers and myself, to send a special word of gratitude to all Christian missions. Let me conclude this with a personal message. I extend my greetings to all our people who are christians on this great feast day. Let us forget the difference in our religion and remember the common brotherhood before God, by dedicating ourselves afresh to the great tasks which lie before us.”

Monday, July 4, 2016

AL'ADUN KASAR HADEJIA... Kashi na Daya (1)



WASU DAGA CIKIN AL’ADUNMU KYAWAWA…
Kasar Hadejia mutanen cikinta suna da Al’adunsu kyawawa wadda suka dace da koyarwar Addinin musulunci, wadannan Al’adu saboda kyawunsu yasa mun taso a cikin kyakkyawan tsari da taimakon Junanmu. Shekaru da dama da suka gabata zakaga mutumin Hadejia bubba da yaro yana da Tarbiyyar idan yaga bubban mutum ya gaidashi, kokuma idan yaganshi da kaya a hannu yaje ya karveshi, wannan Al’ada tana da kyau kuma tayi daidai da tsarin Addinin musulunci. Sannan a shekarun baya duk Unguwar da kaje zakaga tsarin zamantakewarsu akwai ban sha’awa, domin wurin zaman manya daban na yara daban sannan idan zaka wuce Bubban mutum yana zaune zaka cire Takalmi sai ka wuce sannan ka saka. Wani abin ban sha’awa shine Lokacin cin Abinci babu yadda zakaga mutum yaci abinci shi kadai ai haduwa ake mutum huxu ko biyar ake ci tare domin neman Albarka. Wannan ya nuna akwai son juna a tsakaninmu, domin wadda Allah bai bashi ikon yin abinci a gidansa ba to bazai wuni da yunwa ba domin idan yazo Dandali zaici tare da ‘yan-uwansa. Haka yara matasa suma kowa yakan dauko abinci daga gidansu a fito a hadu a ci, wannan muke kira da suna Ciyayya.

ZAMANTAKEWA…
Zamantakewa wata kalma ce da take nuni ga yanayin yadda mutum yake rayuwarsa tare da Abokan zamansa wadda Allah ya hadasu, walau a zaman Makwaftaka ko sana’a da sauransu.

TSARIN SHUGABANCHI…
Shugabanci yana nufin rikon on ragamar Al’umma da basu Umarni da kuma yi musu Jagoranci bisa tafarkin da suka aminta dashi, sannan da tsara musu Dokoki da sasanta tsakaninsu. A Kasar Hadejia tsarin shugabanci ya faro ne tun daga cikin gida inda mutum a gidansa shine shugaba mai shirya komai da kuma bada Doka da Oda, sannan sai shugabancin Unguwa wadda ya kasance kowace Unguwa tana da nata shugaban mai sawa da hanawa da bada umarni shine muke kiransa da suna Mai-unguwa. Duk wani umarni yana fitowa ne daga bakin Mai-unguwa kamar hani da kuma sawa. Shi wannan Mai-unguwa duk abinda ya shafi Unguwarsa shine keda iko akai, kamar Umarni, hani, sasanto tsakanin mutane. Kuma duk Bakon da yazo wannan Unguwa akan kaishi gidan Mai-unguwa ne domin shike da Alhakin yaji abinda ke tafe dashi idan mazauni ne shine da hakkin bashi masauki ta haka ake tsaftace Nagari da Mugu a cikin Unguwa. Baya da Mai-unguwa a gari akwai Malami wadda idan wani Bakon malami yazo wurin Wannan malamin za’a kaishi shi zai bashi masauki sannan yaji Dalilin abinda ke tafe dashi. Haka kuma Idan Bakon dan kasuwa ne akan kaishi Gidan Zangoma wadda shine da hakkin saukar Baki musammam masu saye da sayarwa, shi zangoma shine zai tambayeshi irin Hajojin da yake sayarwa kokuma yake saye domin ya sadashi da masu ciniki. Kaga duk wannan yana nuna muna da kyakkyawan tsari na zamantakewa wadda duk mutumin da ya shigo kasar Hadejia ansan Dalilin zuwansa da kuma abinda yazo yi. A duk lokacin da aka samu hakan shi Mai-unguwa shike da Alhakin sanarwa Bulama sannan Bulama ya sanarda Hakiminsa, shi kuma Hakimi zai sanarda Majalissar Sarki.

Wannan tsarin shugabanci shi ake amfani dashi a kasar Hadejia har lokacin zuwan Turawan Mulkin Mallaka. Koda yake Turawa ma da sukazo sai suka lura cewa muna da kyakkyawan tsari na shugabanci, dan haka sai suka nemi Hadin kan Sarakunanmu ya zamanto zasu bada Umarni ne ga Sarakuna sannan Sarakuna su bada Umarni ga Talakawansu. Turawa sunzo sun samemu da Al’adunmu kyawawa sannan muna da tsari na shugabanci kamar yadda Addinin Musulunci ya tanada mana, wannan dalili yasa Turawa suka samu damar Mulkarmu ba tare da sunsha wahala ba.